Daga Yaseer Haruna
Attajiri Ɗanjuma Adamu Dabo ya fitar da zunzurutun kuɗi Naira miliyan ashirin da biyu, ya bayar domin a nemi mabuƙata da marayu a raba musu, a dukkan ƙananan hukumomi 20 da ke Jihar Bauchi.
Kamar yadda aka tsara rabon, an zaɓi mabuƙata 100 daga kowace, aka ba kowannensu ₦10,000.
Malam Yaseer Haruna a ɗaya daga cikin waɗanda suka gane wa idonsu yadda rabon ya guda. Ya yi addu’ar Allah Ya ƙara wa dukiyarsa albarka, Ya karɓa masa.
Da yake shaida halin kirkin attajirin, Malam Yaseer ya ce: “Wannan bawan Allah ya taɓa faɗa mana cewa, yana mamakin yadda wai masu harkar addini ba za su yi gidauniya ba har sai lokacin siyasa, don an san ana neman takara; duk wanda aka nemi ya taimaka zai taimaka ko don siyasarsa. Ya ce, hakan naƙasu ne, don haka shi ba zai bayar da komai ba har sai bayan siyasa ta wuce, don shi yardar Allah yake nema.”
Ya ƙara da cewa Dokta Ɗanjuma ya taɓa neman takarar Ɗan Majalisar Dattijai a Shiyyar Bauchi ta Kudu bayan rasuwar Malam Ali Wakili, inda sai da aka shiga kotu. Daga ƙarshe ya haƙura don maslaha.
“Allah Ya karɓa masa, Ya yawaita masu tausayin al’umma irinsa,” in ji Malam Yaseer.













