Barkwanci
Kacako!
Wani Bafulatini ne ya hau mota daga cikin Kano zuwa wani ƙauye. Ana cikin tafiya sai yaron mota ya tambaye shi inda zai sauka. Can sai ya ce ya mance sunan garin.
To a cikin motar akwai wani mai zaƙozaƙon haƙora. Da Bafulatanin ya gan shi, sai ya nuna shi, ya ce: “Wallahi sunan garin kamar haƙoran wancan.
Yaron mota ya ce: “Ko Kacako ne?”
Bafulatani ya ce: “Gaskiyarka, Kashako ne!”
~~~
Mai dabara
Wani Babarbare ne ya kai matarsa haihuwa asibiti, ta yi yunƙurin haihuwa ta kasa sai likita ya ce wa mijin ya kawo kuɗi za a yi mata tiyata a cire ɗan.
Babarbare ba shi da kuɗi, ya rasa yadda zai samu kuɗi. Sai ya ce wa likita yana so ya yi magana da matarsa.
Da ya shiga sai ya yi mata magana a kunne. fitowarsa waje ke nan sai ta yunƙura ta haihu.
Likita ya tambaye shi cewa: “Me ka faɗa wa matarka ne?” Sai ya ce: “Na faɗa mata cewa, kina haihuwa zan ƙara aure.”
~~~
Buba da Ilu
Wasu Zamfarawa ne su biyu abokan juna,Buba da Ilu suka zauna suna hira. Can sai Ilu ya ce: “Buba in ka tsinci jikkar kuɗi, nawa kaka ba ni?”
Sai Buba ya ce: “Ilu taro ni ka ba ka walla.”
Ilu ya ce: “Buba ka ba ni taro mana tun da jikkar kuɗin ta maigidanku ta?”
Sai Buba ya ce: “Kai taron na maigidankuna?” Sai fada ya kaure a tsakaninsu, su ne har gaban alƙali.
~~~














Wai tukunna amma tsinci kudinne?