Barkwancin Ƙarshen Mako
~~~~~~~
Jama’a, barkan mu da hutun ƙarshen mako. Ku zo mu ƙyakyata da waɗannan labarun daga Bashir Yahuza Malumfashi, a Jaridar Taskar Gizago:
~~~~~~~
(1) Mun Yi Magana
Wani Badakkare ne ya je yawon neman karnuka a Arewacin Sakkwato. Ya kuwa dace ya samo, a kan hanyarsa ta komawa gida Zuru sai ya bi ta wani garin Zamfarawa. Shi ne gardama ta shiga tsakaninsa da wani Bazamfare. Shi Badakkaren yake ce wa Bazamfare: ”Kai ko a Sakkwato da aka yi magana mun yi magana bare nan umu-umu.” Bazamfare ya ce: “Can Sakkwato me aka ce maka? Kai kuma me ka ce?” Badakkare ya ce: “Cewa aka yi ‘ku tafi daga nan!’ Mu kuma muka ce, mun tafi!”
~~~~~~~
(2) Kinayar Bahaɗeje
Wani Bahaɗeje ne talauci ya kama shi, ya rasa abin da zai yi ya samu kuɗi, sai dubara ta zo masa. Sai da ya bari an biya ma’aikatan gwamnati albashi a Haɗeja, sai ya tafi banki, ya samu wurin na’urar ATM an cika makil ana ta hada-hadar cirar kuɗi. Bahaɗeje kawai sai ya farashe ƙasa, ya yi kamar ya suma, kumfa na fita daga bakinsa. Nan fa mutane suka yo kansa domin taimakonsa, cikinsu sai wani ya riƙa cewa: “Ku samo ruwa a zuba masa domin ya farfaɗo!” Jin za a kwara masa ruwa sai Bahaɗeje ya maƙe murya ya ce: “Ku ƙyale wancan wawan mai batun samo ruwa, idan da agajin ruwa nake so ai bakin Gidan Ruwa zan suma. Ba ku lura da wurin da na suma (banki) ba? Ku agaza da abin da ya dace kawai amma ba da ruwa ba!”
~~~~~~~
(3) Hali Zanen Dutse
Wani ɗan sanda ne yana duba littattafan makarantar ’ya’yansa domin ganin irin ƙoƙarinsu ko akasi, sai ya fara da babban ɗansa. Saboda ɓacin rai sai da ya yi wa yaron bulala 30. Da ya zo kan littafin ƙaramin sai suka ga ya kalli littafin ya fita kawai daga ɗakin. Bayan ya fita sai babban yake tambayar ƙaramin cewa: “Yaya na ga Baba bai doke ka ba, bayan na san kai ma ba ka yi ƙoƙari ba?” Sai ya ce: “Ai Naira ɗari biyu na saka masa a tsakiyar littafin, shi ya sa ya kyale ni.”
~~~~~~~














A gidan ma sai da ya ɗana 😃😃😃
Hahahhahahahahaaha!
Wani Bafulatani ne ya shigo gari, kai tsaye sai ya wuce teburin mai shayi, yace a kulla masa ruwan-bunu a Leda. Ana bashi sai ya wuce shagon probishan yace a bashi abin nan na Leda, da kan shi ya nuna…..mai shago kuwa ya bashi…
Gogan naka ya samu gindin bishiya ya zazzage sachet din nan ya din ga kumbuda baki na kumfa…..Ashe Omon Clean ne!!
Hahahhahhaha! Gaskiya Ɗanfulani ya sha daɗi!
allah me iko yau sebayan shekara 2 da lbr nikuma zanyi comment
malumfashi gsky barawo yafada duk inda kadau uwa aidole yayanta subita inabayanka barawo
Haka ne, ai komai sai Allah ya yi. Ga shi mu ma har yanzu ba mu saka sabon labari ba. Amma ina sha Allahu za mu dawo da zafafan labarai. Mun gode.