Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Allah cikin ikonsa dawwamamme, ya ƙadarta yau ma mun wayi gari Juma’a, cikin ƙoshin lafiya da karsashi. Wannan na nuna mana cewa muna da tabbacin shuɗewar lokaci – daƙika zuwa minti zuwa awa zuwa kwana zuwa mako zuwa wata, daga nan har zuwa shekara.
Da sannu kuma wata rana sai labari, zamaninmu ya shuɗe, sai kuma wasu ba mu ba; kamar dai yadda wasu suka wanzu, suka shuɗe tun kafin zuwanmu.
Ya Allah, yadda muka ga wannan rana ta Juma’a, ka sanya mana albarka a cikinta da bayanta. Ka azurta mu da arzikinka a cikinta da bayanta. Ka rufa mana asiri a dukkan rayuwarmu. Idan lokacinmu ya cika, ya Allah ka azurta mu da cikawa da ingantaccen imani.
Ya Allah, kamar yadda ka yi alƙawarin bai wa manzonka, badadinka, Muhammadu (saw) ceto, mun yi imanin alƙawarinka tabbas ne, ba ya tashi. Ya Allah ka sanya mu cikin cetonsa a ranar ƙiyama. Amin-summa-Amin!
_______________













