KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (2)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

√ Wane Ne Malam Haruna Musa Rugoji?
A rahotonmu na farko, mun tsaya ne daidai inda muka yi wannan tambaya ta sama, domin neman sanin mutumin da a yanzu haka, yake shugabantar wannan hukuma mai matuƙar muhimmanci ga al’umma – KTSTA. Ya kama aiki a matsayin shugaban hukumar a ranar 30 ga Oktoba, 2018 har zuwa yau da muke haɗa wannan rahoto 27-07-2025.
Masu iya magana dai suna cewa, a san mutum a san cinikinsa, ko kasuwa a san dillali. Kamar kuma yadda suka ce, da mai kamar zuwa kan aika, da itace mai gwafa ake yin ƙota. Kamar yadda aka ambata dai, sunansa Malam Haruna Musa Rugoji, (CTN, NPOM, FICEN, FIICA, FlnsTA) – lambobin girma ne da ya mallaka da suka danganci ƙwarewa a fagagen ilimi da sana’a.
An haifi Malam Haruna a garin Malumfashi Jihar Katsina, a ranar 5 ga Fabrairu, 1973. Ya yi karatun firamare a Dudi Primary School Malumfashi, sakandare a Government Day Secondary School Malumfashi, daga nan kuma ya halarci Kwalejin Kimiyya Da Fasaha ta Nuhu Bamalli Polytechnic Zaria, inda ya samu Difiloma a Harkokin Kasuwanci.

Ilimi abokin tafiya, Malam Rugoji bai huta ba, bayan Nuhu Bamalli Polytechnic, sai kuma ya tafi Kwalejin Kimiyya Da Fasaha ta Jihar Kano, inda ya samu shaidar Babbar Difiloma a Ilimin Tsimi Da Tanadi, Hadin Gwiwa da Shugabanci.
Haka kuma ya yi karatun Difiloma ta Musamman a Ilimin Shugabanci, a Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke Bauchi. Daga nan bai huta ba, duk dai domin bunƙasa iliminsa, Malam ya je Jami’ar Bayero Kano, inda ya samu shaidar Digiri Na Biyu, a Ilimin Gudanar Da Sana’a (tare da ƙwarewa a fannin Kasuwanci). Himma ba ta ga raggo – ya sake tafiya Jami’ar Ahmadu Bello Zaria, har ila yau, inda ya ƙara yin wani karatun Digirin na Biyu, a Ilimin Harkokin Sufuri Da Dakon Kaya (2020-2024).
Daga waɗannan manyan makarantu da ya halarta, Malam Haruna ya samu wadataccen ilimin tafiyar da kowace irin sana’a da harkokin kasuwanci, musamman ma harkar sufuri – inda ya fi ƙwarewa a baɗini da kuma aikace. Haka kuma ya samu ƙwarewa a harkar gudanar da shugabanci da mu’amala da mutane. A yanzu haka kuma yana kan ci gaba da nazari da bincike ta fuskar sufuri, dakon kaya, kasuwanci, haɗin gwiwa, bunƙasa sana’a da gudanarwa a zamanance, ta fuskar amfani da fasahar zamani, kamar yadda ake gudanarwa a manyan ƙasashen da suka ci gaba. Wannan ke ƙara tabbatar da cewa, an ajiye ƙwarya a daidai burminta, da aka ba shi shugabancin wannan hukuma ta sufuri ta Jihar Katsina (KTSTA).
A can baya, kafin Malam Haruna ya kama aiki a matsayin Shugaban Hukumar Sufuri ta Jihar Katsina, ya yi aiki da sana’o’i, ko dai na ƙashin kansa ko kuma na gwamnati. Misali, Malam Rugoji ya yi aikin koyarwa a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Hassan Usman Katsina Polytechnic kuma babu shakka ya cika dukkan sharuɗɗa da ƙa’idojin aiki, tsakaninsa da hukumar makaranta da ɗalibai da sauransu – sai san barka.

Haka kuma, daga ranar 13 ga Agusta, 2018 zuwa 30 ga Oktoba, 2018, Gwamnan Jihar Katsina a lokacin, Alhaji Aminu Bello Masari ya naɗa shi muƙamin Shugaban Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Katsina (SEMA). A nan ma, tabbatattun shaida sun shaida yadda ya gudanar da aikin hukumar cikin nagarta, gaskiya da adalci, inda a cikin ƙankanen lokacin da ya shugabanci hukumar, aka ga gagarumin canji da biyan buƙata. A ɓangaren kasuwanci kuwa, ya taɓa zama Janar Manaja na gidan man Loyal Abdul Son Petroleum Nig. Ltd. na Shiryar Gombe (2010-2015).
In sha Allahu a rahoto kashi na 3, za mu ƙarƙare bayani game da Shugaban Hukumar Sufuri ta Jihar Katsina, Malam Haruna Musa Rugoji, daga nan kuma mu shiga batutuwan da suka shafi hukumar kai tsaye. A ci gaba da biyo mu.
_______________
Bashir Malumfashi, shi ne Editan Mujallar Taskar Gizago (online)













