Baffa Hotoro Ka Ci Amanar Ilimi
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Akwai takaici da ƙunar zuciya, mutum ya ga abin da bai kamata ba daga hannun wanda ya kamata a ce ya san ya kamata.
Na ci karo da wani faifan bidiyo a Soshalmidiya, inda na ga matashin malamin Musulunci, Baffa Hotoro Kano yana kausasa harshe, cikin izzar rashin ta ido, yana antaya antayayyun kalamai a kan marigayi Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi. Ba sai na maimaita kalaman ba a nan saboda muninsu kuma ina da tabbacin mutane da dama sun ji kalaman nasa a wannan saha da waninta.
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Haba Malam, don Allah ina ilimin naka yake, ina ka manto Sunnar Manzon Allah (saw)? Maganar gaskiya ka ci amanar ilimi kuma ka cutar da Sunnar Manzon Allah (saw). Ya kamata ka gaggauta tuba, ka gaggauta fitowa fili ka nemi gafarar iyalan marigayi, ka nemi gafarar miliyoyin Musulmi da suka ji ba daɗi daga munanan kalamanka.
Malam Hotoro, na san ka san da umurnin da ke cewa: “Ka tunatar, tunatarwa tana amfanar muminai.” Don haka ina kyautata maka zaton cewa kai mumini ne.
Bisa ga haka, bari in tunatar da kai wannan hadisin na Manzon Allah (saw) daga Sahih Bukhari, mai lamba 1393, wanda ya yi hani da tozarta mamata: “Kada ku zagi matattu, domin sun riga sun kai ga abin da suka aikata.”
Ko ba komai, marigayi mahaddacin Alkur’ani ne mai girma. Ya karanta kuma ya karantar da shi. Ko ba komai, marigayi ya yi tsufan da ya yi kakan-kaka da kai kuma Allah ya fitar masa da furfura, wacce Manzon Allah (saw) ya ce a girmama mai ita. Ko don waɗannan dalilai kaɗai, bai kamata ka kausasa harshe a kansa ba. Da ma shiru ka yi da bakinka, wallahi da ya fi alheri.
Malam Baffa Hotoro, ina yi maka da ni kaina da dukkan al’ummar Musulmi nasiha. Mu ji tsoron Allah, mu kiyaye harshenmu, mu kiyaye amanar ilimi, mu kiyaye tozarta bayin Allah.
Ya Allah ka yi mana uzuri, ka kawar da Shaiɗan daga hanyarmu, ka yafe mana zububbanmu. Amin-Summa-Amin!
_______________












