Neman Hanyar Gaskiya A Addini
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
A wannan zamani da muke ciki, al’amura musamman na addini sun rikice. An wayi gari da mabambantan firƙoƙi da malamai iri-iri, masu fahimta iri daban-daban.
A irin wannan yanayi, idan mutum bai natsu ba, idan bai nemi agaji daga Allah ba, zai iya zama tamkar ƙwallon ƙafa, domin kuwa za a yi ta shura shi kusurwa-kusurwa.
Don haka ya kai ɗan uwa, a matsayinka na Musulmi, mai neman tsantsar gaskiya da gaskiya a addini, ya zama dole ka natsu, ka nemi ilimi da gaske. Ka buɗe tunaninka ka yi karatu mai yawa. Ka buɗe kunnuwanka ka yi saurare mai yawa. Ka tsarkake zuciyarka da kyakkyawan imani da Allah, tare da roƙonsa ya ɗora ka a kan gaskiya.
Duk abin da ka karanta na addini, duk fatawar da ka samu daga malamanka na addini, sai kuma ka zauna ka saita tunaninka. Allah ya ba ka ƙwaƙwalwa ne domin ka yi tunani, ka bambance mai kyau da marar kyau.
Allah (swt) a cikin Alkur’ani mai girma, Suratu Ṣād, aya ta 29 ya ce: “Wannan littafi (Alkur’ani) ne da Muka saukar maka mai albarka ne, domin su yi tadabburi (zurfin tunani) a kan ayoyinsa, kuma su sami tunatarwa masu hankali.”
Wannan ya ishe mu zama ma’aunin gane addini na gaskiya daga bara-gurbi. Madamar kana amfani da zurfin tunaninka wajen tantance gaskiya, kai daga jin fatawar da ta inganta, za ka gane. Haka ma da zarar ka ji wata kwaɓar, za ka fahimta.
Jama’ar Allah, ku ƙara mana da wasu shawarwarin a Comment Section. Shin wane mataki ya kamata mu ɗauka a yayin da muke neman sahihiyar hanyar gaskiya a addini?
__________













