SUBHANALLAHI:
‘Yan Sanda Sun Kulle Danladi Z. Haruna
~~~~~~~
A bara cikin watan Agusta, tsautsayi ya haifar da shiga ta gadirum a karo na farko. Ni da nake daya daga wadanda aka yi wa sata, sai mutanen unguwa ke zargin wai na saki barawon da suka kama. Magana har gaban kotu. Mai shari’a ya kori karar saboda rashin abin kamawa, tare da taimakon lauyoyi uku da suka tsaya min.
Tun farko a wajen ‘yansanda bayan doguwar magana, aka jefa ni gadirum saboda wai kada na gudu. Ina shiga na tarar da mutum bakwai kowa a takure. Sai dai cikinu akwai wani ƙato da ya zage ƙwanji yana ta jibgar wani ƙaramin yaro. Shi kuma yaron yana ta tsiwa da zage-zage. Ƙaton nan dukansa yake tun ƙarfinsa amma babu wanda ya kula cikin mutane da ke wajen. Wani ma na can gefe ya duƙunƙune. Sai idan titirniyar ta faɗo kansa ne yake kaucewa gefe daya yana gurnani.
Abinka da sarkin kankanba. Da ganin ana irin wannan aika-aika sai na tsunduma ciki ka’in da na’in. Da farko na soma da zagin yaron ina masa tsawa kan ya yi shiru shi kuma yana dagewa. Sai nima na rufa na bi sawun wanda ke jibgar tasa. Amma fa dabara na yi, idan katon ya kai naushi sai na tare shi. Ni kuma sai na kai wa yaron bugu mara zafi. Shi kuma yaron sai ya ture ni.
Duk lokacin da na tare dukan katon nan, sai na ji kamar buhun siminti aka jefo min. Duk da haka na hana bugun nasa ya samu yaron. Ni kuma sai na takarkare kamar gaske na kai wa yaron naushi amma bana yarda na same shi. Ina yi ina surutu ina aibata yaron da yawan tsiwa.
Da ƙaton nan ya fahimci abin da nake yi, sai cakumi ƙuguna. Ni dai ban san yadda aka yi ba, sai na ji an yi sama da ni kamar filfilwa. Na ji an yi gaba da ni, sai na ji an dawo da ni baya. Sai ga ni jikin wanda ya takure din nan kaina ya naushi hakarkarinsa.
Na yi zumbur na mike tsaye, mu uku duka kowa ya galabaita sai huci yake kamar zakaran da ya kasa ƙoto. Na dubi yaron nan fuskarsa jina-jina duk ta kumbura amma sai tsiwa yake yi bai fasa ba. Shi kuma ƙaton nan sai hararata yake yi yana cewa, “wai kai taya ni dukansa kake yi ko kuwa hana ni kake yi?” Na yi farat na ce duka biyun.” Na ce, “yanzu kai da girmanka, yaushe za ka ɓatawa kanka lokaci wajen dukan wannan dan tamilon?”
Ya ce, “ba ka san shegen yaron nan ba ne.” Nan ya soma bani labarinsa. Sai na fahimci ashe wannan ƙaton ɗan sanda ne mai mukamin Sajen, ya yi laifi aka sakaya shi. An ce ba zai fita ba sai yayi kwana bakwai. Shi kuma yaron, sata ya yi. Kuma a waje sun san juna suna takun saƙa. Haduwarsu a ciki ta sa yake masa gorin shi ma ga shi nan an kawo shi inda yake kai mutane. Tun da suka fara fadan babu wanda ya ce musu kanzil a tsararrun nan sai ni daga zuwa na. Sai dai lokaci zuwa lokaci ‘yan sanda na lekowa su yi musu tsawa.
Yana ba ni labarin abin da ya haɗa su ina goyon bayansa. Hira ta yi nisa tsakaninmu, sai aka manta da dukan yaro muka shiga hirar duniya. Ya riƙa gaya min irin manyan iyayen gidansa. Ni kuma ina ce masa na sansu. Wasu na san su, wasu kuma ban san su ba.
Zamana a cikin gadirum din bai wuce awa daya da mintuna ba, na sa aka sayo mana abinci da biskit da ruwa muka ci muka sha. Sanan na tilastawa yaron nan ya ba wa sajan hakuri.
Lokacin da zan fita, tsararrun nan suna mini godiya, sai yaron ya ce, “oga Allah ya sa gobe ka dawo.” Na juyo da sauri na ce masa, “bakinka ya sari danyen kashi.”
Wannan ne karon farkon shiga ta gadirum a tsawon rayuwata.
~~~~~~~












