Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ƙaddamar Da Babban Aikin Samar Da Ruwa
Daga Abdullahi Salisu

•••••••
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa ya kafa tubalin gina kashi na biyu na aikin samar da ruwa daga dam ɗin Zobe zuwa wasu sassa na jihar.
Bikin kafa tubalin aikin, wanda ya gudana a jiya Laraba, a maharbar ruwa da ke Kafinsoli cikin Ƙaramar Hukumar Kankiya, wani muhimmin mataki ne na gwamnatinsa domin tabbatar da samun ingantaccen ruwan sha ga jama’ar jihar.
Aikin, wanda ake sa ran zai amfanar da dubban jama’a, zai shafi garuruwan Karofi, Raɗɗa, Kafinsoli, Tafashiya, Kankiya, Koda-Charanchi, ‘Yarranda, Tashar Albasa, Are, Ci Ka Ƙoshi, Faduma, Tudun Ƙadiri, Rijiya Mai Siminti, Lambar Rimi, Abukur, Tashar Bala da Ɓatagarawa.
Waɗannan garuruwa suna a cikin ƙananan hukumomin Dutsin-ma, Kankiya, Kusada, Charanchi da Ɓtagarawa. Wannan aikin yana daga cikin manyan ayyukan Gwamnatin Dokta Raɗɗa na kammala muhimman ayyuka da za su kawo sauyi mai ma’ana ga rayuwar jama’a a faɗin Jihar Katsina.
Yayin jawabinsa a wajen taron, Gwamna Dikko Umar Raɗɗa ya jaddada cewa gwamnatinsa ta ƙuduri aniyar magance matsalar ƙarancin ruwa a jihar ta hanyar saka hannun jari mai yawa da samar da tsarin kula da albarkatun ruwa mai ɗorawr. Ya bayyana cewa kammala aikin Zobe zai taimaka wajen rage matsalolin ƙarancin ruwa da kuma inganta rayuwar al’umma.
Kwamishinan Ma’aikatar Ruwa ta Jihar Katsina, Hon. Bishir Gambo Saulawa ya bayyana cewa aikin mataki na 1B ya haɗa da gina bututun tura ruwa, manyan ma’adanan ruwa, da tsarin rarraba ruwa zuwa garuruwa. Ya ce ma’aikatar tana aiki tare da Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa aikin ya kammalu cikin lokaci da kuma bisa ƙa’idar da aka tsara.
Shugaban Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Dokta Tukur Tingilin, ya yaba wa Gwamna Raɗɗa bisa hangen nesa da jajircewarsa wajen farfaɗo da tsoffin ayyukan ruwa a jihar. Ya ce wannan aiki zai taimaka wajen ƙara samun tsaftataccen ruwa, rage yaɗuwar cututtukan da suka shafi ruwa da kuma bunƙasa harkokin noma da tattalin arziki a yankin.
Taron ya samu halartar shugabannin ƙananan hukumomin Dutsin-ma da Kankiya da Kusada da Charanchi da Ɓatagarawa. Haka ma sarakunan gargajiya daga yankunan da aikin zai amfana da mambobin majalisar zartarwa na Jihar Katsina da jami’an ma’aikatar ruwa da sauran muhimman baƙi, duk sun samu halarta.
_______________













