A 2027 Talakawan Najeriya Za Su Nuna Wa Tinubu Iyakarsa – Aminu Waziri
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Dokta Aminu Waziri, jigo a Jam’iyyar SDP a Jihar Katsina ya bayyana cewa idan Allah Ya kai mu zaɓen shekarar 2027, talakawan Najeriya za su maida wa Shugaba Tinubu da biki, inda za su kayar da shi, su zaɓi wani shugaba da ya fi dacewa.
Kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Facebook, ya ce, Shugaba Tinubu ya wulaƙanta takakawan Najeriya, ya tura su cikin uƙuba da matsalolin rayuwa da suka haɗa da yunwa da rashin tsaro, don haka ba za su ƙara zaɓen shi a karo na biyu ba.
” A 2027, zaɓen ba shi da alaƙa da yawan gwamnonin jihohi da jam’iyya ke da su. Domin kuwa a zaɓen Shugaban Ƙasa na 2023, APC ta rasa jihohin Nasarawa, Kano, Kebbi, Kaduna, Legas, Imo, Katsina, Yobe, Gombe, Ebonyi, Cross River da Filato ga jam’iyyun adawa.”
Ya ƙara da cewa, dukkanin waɗannan jihohin suna ƙarƙashin gwamnonin APC ne a wancan lokaci amma duk da haka suka kasa cin kujerar Shugaban Ƙasa.
“Kuma ai Okowa yana Gwamnan Jihar Delta amma Peter Obi ya lashe wasu jihohi ba tare da yana da gwamna a jam’iyyarsu ta LP ba,” in ji Waziri.
Ɗan siyasa Aminu Waziri ya jaddada cewa, wannan ya faru ne a 2023 lokacin da ‘yan Najeriya ba su fuskantar yunwa da wulaƙanci irin na yanzu da Shugaba Tinubu yake gallaza masu.
“Don haka, babu wani talaka da zai damu, koda dukkanin gwamnonin jihohi 36 ne suka shiga APC, za su sha kaye tare a 2027, domin kuwa sun gaji da mulkin danniya da zalunci.
“Zaɓen 2027 zai kasance ne tsakanin talakawa a gefe ɗaya da Shugaba Tinubu tare da manyan tawagarsa ta baragurbi, masu zaluntar talakawa. Allah ya ba Najeriya nasara, Amin.” In ji Dokta Aminu Waziri.












