ƊAN IYA MAI ALLAH
_____
Sadaukarwa ga Ɗan’Iyan Galadiman Katsina, Alhaji Shehu Musa Ɗankano, a yayin da ya cika shekara 70 a yau Lahadi 22-10-1446 (Hijiriyya), 20-04-2025 (Miladiyya).
_____
Allahu mun maka godiya,
Mun ƙara yi maka godiya.
Manzonmu ya Nurulhuda,
Mun yo salati gaba ɗaya.
Ɗan’Iya mun maka jinjina,
Barka da himma da juriya.
Mun yabe ka da ƙoƙari,
Malam Nomau kake tun jiya.
Mun yabe ka da himma,
A fagen mulki kai ka iya.
Mun san ka kai ba za’ida,
Ba ka lasar ta haramiya.
Burinka duk a yi hanƙuri,
A cikin lamurran duk duniya.
Kai uba ne gun al’umma,
Burinka a zauna lafiya.
Kai ishara ka daɗa,
Mu kama ilimi bai ɗaya.
Mun zamto girmama juna,
Kullum mu zauna lafiya.
Ga addu’a don Ɗan’Iya,
Allah ƙara imani da lafiya.
__________
© Bashir Yahuza Malumfashi,
Lahadi, 22-10-1446 (Hijiriyya)
20-04-2025 (Miladiyya)
__________












