IDAN APC TA AMSHI KANO: INA MAKOMAR SARAKUNA BIYU?
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Wani babban al’amari da ya daɗe yana ɗaukar hankalin al”umma a Jihar Kano, shi ne tataɓurzar Masarautar Kano, inda sarakuna biyu ke ta sañatta-juyatta da juna.
A gefe guda, akwai Sarki Aminu Ado Bayero, wanda Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta sauke. Sai kuma ɗaya gefen, na Sarki Muhammadu Sanusi II, wanda gwamnatin ta dawo da shi bisa karaga, kasancewar tsohuwar Gwamnatin Jihar Kano, a ƙarƙashin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta sauke. Al’amarin da ya kawo rarrabuwar kai, ya kawo hautsini, kuma ake ta fafata Shari’a a kansa.
Babban abin da ya haifar da wannan matsala shi ne, yadda aka samu al’amarin na Masarautar Kano ya faɗa komar siyasa da ‘yan siyasa. A lokacin da Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta NNPP, bisa jagorancin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ke goyon bayan Sarki Muhammadu Sanusi II, ita kuma Gwamnatin Tarayya ta APC, bisa sahalewar Shugaban Jam’iyyar APC kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, take goyon bayan Sarki Aminu Ado Bayero.
A yanzu da ake tsammanin wani sabon al’amari zai gudana a siyasance a Jihar Kano, akwai yiwuwar kawo ƙarshen wannan taƙaddama da ta baibaye Masarautar Kano. Wannan kuwa shi ne, jita-jita ta yi tsauri, cewa Madugun Kwankwasiyya, Injiniya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso zai koma Jam’iyyar APC, inda zai haɗe da tsohon mataimakinsa, wanda suka raba gari da juna, wato Abdullahi Umar Ganduje.
Kasancewar ɗaki ba ya tashi ragaya ta zauna, ana sa ran idan Kwankwaso ya shiga APC, to kuwa Gwamna Abba Kabir Yusuf ma, tare da ayarinsa ‘yan Keankwasiyya su ma za su koma APC. Ke nan Jihar Kano za ta koma hannun Gwamnatin Tarayya, ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Hakan zai sa a ɗinke, a zama ɗaya – babu adawa ko tsama ke nan a siyasance.
Idan haka ta faru, to ina makomar sarakunan nan biyu da ke gwara kan juna, wato Sarki Sanusi da kuma Sarki Aminu? Shin za a dawo da sauran masarautu biyar ne da aka soke, shi Aminu ya koma Sarkin Bichi, a bar Sarki Sanusi da ƙwaryar Kano, ko kuwa?
Tabbas dai idan Gwamnatin Tarayya ta APC ta karɓe Kano, dole ne a samar da matsaya game da matsalar Masarautar Kano.
Al’ummar Allah, me kuke zaton zai faru da sarakunan nan biyu? Ku bayyana ra’ayinku a Comment Section!
_______________
Bashir Yahuza Malumfashi,Taskar Gizago.












