Shawara Ta Fi Muhawara
SHAWARA
TA FI
MUHAWARA
Kafin ka yi magana,
Yaka ka zo nan ɗan uwa.
Sai ka lura ka gane,
Maganar ina taka zuwa?
Magana zarar bunu ce,
In ta fita ba ta komuwa.
Magana iri biyu ce,
Muddin za ka batuwa.
Wata kam alheri ce.
Alherin shi ka samuwa.
Akasin ta sharri ne,
Sharrin shi ka wanzuwa.
Ɗan uwa ka lura ka gane,
Batun nan sai da kintsuwa.
‘Yar uwa ki zam dubawa,
Har kullum sai da natsuwa.
Duk idan za ku aikata,
Wani aiki duk mai bazuwa.
Shi ma a nan iri biyu ne,
Babu na ukkunsa ‘yan uwa.
Wani kam mai kyawu ne,
Na biyun mai sanya damuwa.
Shi hali zanen dutse,
Kulluyaumin ba ya goguwa.
Sai mu zamto yin kirki,
Domin shi ne gyaruwa.
Mu tsare haƙƙin addini,
Shi ne turba ta shiryuwa.
Mu yi soyayya don Allah,
Ita ce ribar da ka yaɗuwa.
Mu riƙe Manzon Allah,
Almusɗafa mai bagaruwa.
Hassada mugun ciwo,
Mu guje ta sai mu tohuwa.
Mu zam yin adalci,
Shi ne jigo a rayuwa.
Gaskiya babbar hanya,
Ita ce ke kai mu datuwa.
Mu taimaki junanmu,
Haɗin kai kama hannuwa.
Allah sanya mu mu dace,
Ka sassaita mu rayuwa!
__________
© Bashir Yahuza Malumfashi
Jumu’a, 24-12-1441 (Hijriyya)
14-08-2020 (Miladiyya)













