• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, April 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

SADAUKARWA: Tinubu Tsaye Yake Ga Manufofin Najeriya Da Afirka – Minista Idris

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
October 22, 2023
in Labarai
0
SADAUKARWA: Tinubu Tsaye Yake Ga Manufofin Najeriya Da Afirka – Minista Idris

Alhaji Mohammed Idris (na 5 daga hagu) tare da sauran manyan baƙi a wajen walimar da aka yi a Ofishin Jakadancin Angola a daren Alhamis

3
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

SADAUKARWA: Tinubu Tsaye Yake Ga Manufofin Najeriya Da Afirka – Minista Idris

Daga Wakilinmu

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026

~~~~~~~
Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa sadaukar da kai da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi bai tsaya ga Nijeriya kaɗai ba, har ma da dukkan nahiyar Afrika.

Ya ce: “Tun daga lokacin da ya kama aiki, an gan shi sosai a faɗin duniya yana yayata manufofi da burukan Nijeriya da ma nahiyar Afrika.”

Ministan ya faɗi haka ne a wurin wata walimar cin abincin dare, wadda Ofishin Jakadancin ƙasar Angola ya shirya a Abuja a ranar Alhamis.

Ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu yana da shauƙin ganin ya inganta mu’amalar da ke tsakanin Nijeriya da sauran ƙasashen Afrika, ciki har da Angola.

Idris ya ce yanzu ana kallon Shugaban Ƙasa a matsayin uba a faɗin Afrika, wanda ke jagorantar ƙasar da ta fi kowace yawan jama’a da ƙarfin arziki a nahiyar.

A cewar sa, wannan ne ya sa aka naɗa Tinubu Shugaban Ƙungiyar Ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), jim kaɗan bayan an rantsar da shi a matsayin Shugaban Ƙasa.

Ya ce: “A jawabinsa a wajen babban taron farko da ya halarta na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) a watan jiya, ya yi magana mai gamsarwa ƙwarai kan dalilan da suka sa Afrika take buƙatar sauran ƙasashen duniya su yi mata adalci, da abin da ya sa ci gaban duniya yana tattare ne da ci gaban Afrika.

Ya ce, “Wato dai manufa, idan har duniya ta ɗauki batun samun ci gaba da gaske, to tilas ne kuma ta ɗauki batun ci gaban Afrika da gaske.”

Ministan ya ƙara da cewa mafarkin Shugaba Tinubu da burinsa su ne ƙasashen Afrika su haɓaka dangantaka mai zurfi da ƙarfi a tsakaninsu wanda “zai ba da dama ga nahiyar ta samu matsayin da ya fi na da girma da ƙarfi a fagen duniya da kuma samun dama mafi girma wajen samun ‘yanci mai ɗorewa da arziki. Duk abin da ya gaza kan wannan, to ba za mu yarda da shi ba.”

Ya yi la’akari da cewa idan har ba a haɗa kafaɗa aka yi mu’amala da haɗin kai tare ba, Afrika ba za ta cin ma nasarar warware matsalolinta ba.

Idris ya ce: “Ƙoƙarin magance ɗimbin ƙalubalen da ke fuskantar nahiyar a wannan zamani – irin su rashin tsaro, fatara, rashin aiki, labarai marasa daɗi, ƙarancin hada-hadar kasuwanci a tsakanin nahiyoyi, da sauransu – duk yana buƙatar yin aiki kafaɗa da kafaɗa a matakin yanki da na nahiya baki ɗaya.

“Duk da yake akwai bambance-bambancen harsuna da al’adu da tsarin zamantakewar al’umma da na siyasa, tilas ne mu samo hanyoyin da za mu amince da su domin gabatar da matsaya ɗaya kan al’amurran da suka shafi mu su waye a matsayin nahiya, da abin da muke so mu cin ma wa a dukkan ɓangarori na rayuwa.

“Tilas mu haɗu mu tattaro tunani kan batun ci gaban ƙasa, kafa masana’antu, cinikayya, samar da aikin yi, da kuma matsayin nahiyarmu a ƙarni na 21. Yanzu haka an yi nisa wajen aiki kan hakan, don a fitar da matsaya ɗaya haɗaɗɗiya wadda za a yi aiki da ita a matakai daban-daban.”
~~~~~~~

Previous Post

Bago Ya Taya Ndace, Sabon Shugaban VON Murna

Next Post

TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Bura women Celebrate Bukar Usman at 83
Labarai

Ƙungiyar Matan Al’ummar Bura Sun Karrama Dr. Bukar Usman Bisa Cika Shekaru 83

January 9, 2026
Next Post
TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

TATTAUNAWAR KHALID IMAM: Zuwa Ga Malam Bashir

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

BUWDA is the Pride of Bura People, Humanity in General – Dr. Bukar Usman

BUWDA is the Pride of Bura People, Humanity in General – Dr. Bukar Usman

April 14, 2025
Humility and Gentility: My Encounter with Dr. Bukar Usman

ZIYARA GA BUKAR USMAN: Ganawa Da Mutum Mai Karimci Da Tawali’u

October 19, 2023
Dogo Na Magayaƙin Kano Ya Angwance

Dogo Na Magayaƙin Kano Ya Angwance

July 16, 2023
TSOKACINMU NA YAU (09)

TSOKACINMU NA YAU (09)

March 9, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.