• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, June 25, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 31, 2023
in Adabi
0
YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Littafin Yamtarawala

42
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Littafin wasan kwaikwayo mai taken “Yamtarawala – The Warrior King (Yamtarawala – Jarumin Mayaƙin Sarki) ya kama hanyar lashe Gasar Adabi ta bana, wadda Kamfanin Sarrafa Iskar Gas na Najeriya (NLNG Limited) ke shiryawa duk shekara.

Related posts

Maryam ‘Yar Aljanna (2)

Maryam ‘Yar Aljanna (2)

June 22, 2026
Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

June 21, 2026

Littafin, wanda marubuci kuma ɗan jarida Henry Akubuiro ya rubuta, ya samu nasarar tsallake shingen alƙalan gasar, inda ya kasance ɗaya daga cikin uku da za su fafata domin fitar da na ɗaya da na biyu da kuma na uku.

A ranar Talatar da ta gabata (29-08-2023) ce, Shugabar Kwamitin Gasar, Farfesa Akachi Adimorah ta sanar da sunayen littattafan guda uku. Sauran biyun sun haɗa da littattafan wasan kwaikwayo mai taken “For Grit” na marubuci Obari Gomba da kuma “The Ojuelegba Crossroads” wanda Abideen Abolaji Ojomu ya rubuta.

Kamar yadda kwamitin ya bayyana ingancin littattafan uku da suka yi nasara, ya ce tsarin wasannin kwaikwayon sun ciri tuta, musamman ta fuskar zubi da tsari, zaɓen kalmomin da suka dace da al’ada da kuma ingancin labari, wanda za a iya nunawa a aikace, a fim ko a daɓe. Ya ƙara da cewa littattafan sun cancanci ƙima ta musamman, a fagen adabi, waɗanda suka haɗa dukkan wata ƙwarewa a sarrafa alkalami da hikima, irin dai wadda kwamitin na Gasar Rubutun Adabi ta Najeriya ke buƙata.

Shugabar Kwamitin ta ce, alƙalan gasar sun yaba wa littafin “For Grit” da cewa babban wasan kwaikwayo ne da ya gamsar fiye da ƙima. Tsarin warware jigon labarin yana kama hankali, tsarin bugun littafin ya ƙayatar sosai.

Game da littafin “The Ojuelegba Crossroads” kuwa Farfesa Akachi ta ce alƙalan sun gamsu da shi sosai. Sun ce ya kawo bayanan da suka danganci zamantakewar al’umma da siyasa. Irin yadda marubucin ya tunkari bayyana faɗi-tashin al’umma na yau da kullum, da yadda suke ɗaukar matakan daidaita rikitattun al’amuran rayuwarsu domin dacewa, su ne suka inganta littafin, suka ba shi babbar daraja.

Da Shugabar Kwamitin ta zo bayani game da littafin “Yamtarawala – The Warrior King” na Henry Akubuiro kuwa, cewa ta yi: “Littafin ya ɗauki hankalin alƙalan gasar saboda tsarinsa mai hawa da sauka da nuna gwanintar wasan kwaikwayo. Yadda aka tsara shi bisa dacewa da inganci, zai sauƙaƙa ɗabbaƙa shi a aikace, a daɓe ko ma a allon fim. Irin yadda marubucin ya warware ƙunshiyar labarin, yana riƙe mai karatu cikin ƙayatarwa da saka nishaɗi.”

Baya ga kwamitin shirya gasar, marubutan uku da suka yi nasara sun samu yabo da jinjina daga ƙungiyoyin marubuta da ɗaiɗaikun mutane daban-daban.

A nata ɓangaren, Ƙungiyar Matasan Marubuta ta Najeriya (SYNY), taya murna ta yi gare su, bisa gagarumar nasarar da suka samu. A wani jawabi da shugaban ƙungiyar, Wole Adedoyin ya fitar, ya ce: “A matsayinmu na ƙungiyar da ta sadaukar da kanta wajen rainon matasan marubuta a Najeriya, muna alfahari da nasarar da Dokta Obari Gomba, Mista Henry Akubuiro da Mista Abideen Abolaji Ojomu suka samu. Wannan nasara da suka samu, abu ce mai ƙarfafa gwiwa ga marubuta masu tasowa, wajen yi masu jagora zuwa maida hankali ga ayyukan ƙirƙira domin samun ɗaukaka.

“Ƙungiyarmu na taya marubutan uku fatan samun kyakkyawar nasara a ƙarshen gasar, inda za a fidda zakara. Kasancewar wannan gasa tana da kyakkyawan tarihi dangane da ɗaga martabar nagartattun ayyukan adabi, muna da yaƙinin cewa, duk wanda ya yi nasarar zama zakara daga cikin waɗannan zaƙaƙuran marubuta uku, zai cancanci duk wata Karramawa daga wajenku.”

Ita dai wannan gasa da Kamfanin NLNG ke ɗaukar nauyin gudanarwa duk shekara, tana karrama zakaran da ya zo na ɗaya da kyautar Dala dubu 100.

A gasar ta bana, adadin littattafan wasan kwaikwayo 143 suka fafata, inda marubuta uku suka yi nasarar zuwa shingen ƙarshe. Kamar yadda kwamitin gasar ya bayyana, za a sanar da zakaran zakaru a ranar 13 ga Oktoban bana, a wani ƙwarya-kwaryan biki.
~~~~~~~~

Previous Post

Littafin Bango Ya Tsage: Takaitaccen Tsokaci Da Shawara

Next Post

NASIHAR JUMU’A: Daga Sheikh Aliyu Said Gamawa

Related Posts

Maryam ‘Yar Aljanna (2)
Adabi

Maryam ‘Yar Aljanna (2)

June 22, 2026
Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa
Adabi

Dakta Bukar Usman Zai Gabatar Da Sharhin Littafin Tarihin Al’ummar Lassa

June 21, 2026
Maryam ‘Yar Aljanna
Adabi

Maryam ‘Yar Aljanna

June 20, 2026
Next Post
Lallai Hukuma Ta Tallafa Wa Marubuta Domin Yaƙar Jahilci – Sheikh Gamawa

NASIHAR JUMU'A: Daga Sheikh Aliyu Said Gamawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Hattara Da Munafukan ‘Yan Siyasa A Jihar Kebbi

Hattara Da Munafukan ‘Yan Siyasa A Jihar Kebbi

November 19, 2025
JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

February 24, 2026
Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

Najeriya 2027: Matsalolin Da Za Su Iya Wargaza Takarar Obi Da Kwankwaso

March 29, 2026
Janar Magashi Bai Mutu Ba

Janar Magashi Bai Mutu Ba

June 24, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • ACF Endowment Fund Sets Agenda for Transparency, Education and Empowerment in Northern Nigeria
  • Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo
  • Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

ACF Endowment Fund Sets Agenda for Transparency, Education and Empowerment in Northern Nigeria

ACF Endowment Fund Sets Agenda for Transparency, Education and Empowerment in Northern Nigeria

June 24, 2026
Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

June 23, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.