Bulalar Zumunci!
~~~~
Da sunan Allah na fara,
Yabon Manzo ni na ƙara,
Neman fatahi ba guba ba.
~
Ni ne Bashirun Yahuza,
Malumfashi babu biza,
Ɗan uwanku ne ba da wai ba.
~
Ya jama’a ni nai kiran ku,
Don nasiha babu tsurku.
Ku saurara ba da gundura ba.
~
Lokacin yau ya yi tsatsa.
Idonmu duk ya yi kwantsa.
Mu zam nazari ba shiru ba.
~
Baiwar nan ta fa haife,
Uwargijiyarta tun safe,
Mu duba tsaf ba jugum ba.
~
Gaskiya ta ƙaurace mu,
Ƙarya ta kusance mu,
Mu gyara ba da jinkiri ba.
~
Mu ne kwaɗayi tamkar ƙuda.
Mu ne kaushi tamkar kada.
Mu sanya kula ba jira ba.
~
Manyanmu sun sauka layi.
Matasa sun shaƙi yayi.
Taƙadarci duk ba mu bari ba.
~
Matanmu kam sai du’a’i.
Kullum a wurinsu sai jafa’i.
Shegantaka ba su daina ba.
~
Masallatai mun cika fal.
Coci-coci an mamaye sal.
Ga cutar juna ba mu bari ba.
~
Ya Allah ta roƙo muke,
Ka yafe mana tuba muke.
Neman Rahama ba mu bari ba.
~~~~~~~
© Bashir Yahuza Malumfashi
Lahadi, 19-01-1445 (Hijriyya)
06-08-2023 (Miladiyya)
~~~~~~~













