Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (1)
Daga Yahuza Malumfashi

Gabatarwa:
Da sunan Allah mai Rahama mai jin ƙai. Tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammadu (saw).
Bayan haka, na ƙuduri aniyar gabatar da tsokaci game da wannan al’amari mai take a sama, dangane da yunƙurin da na gani, na wasu bayin Allah da suka daddage wajen samar da wata fitina ko ruɗani a cikin al’ummar Arewa.
Babban dalilin da ya sa zan tofa albarkacin bakina kan wannan sha’anin shi ne saboda wasu salelai da na ankara da su daga wasu daga cikin masu ƙumajin samar da wata ƙungiya wai ta kishin Hausa ko kuma ta Hausawa zalla – salelan da na ankara da cewa sun yi bambarakwai, wai kiran Salla da usur.
A wannan muƙala, idan Allah ya yarda zan yi ƙoƙarin bijiro da tsokaci, tare da sharhi, domin saita hanya. Akwai zargi mai ƙarfi na cewa, ‘yan ƙungiyar Ba-Zata ne suka shirya shigar bututu domin wargaza zaman lafiya da aminci tsakanin al’ummar Arewa. Kan haka za mu bijiro da tambayoyi kamar, shin su wane ne ‘yan Ba-Zata? A wannan zamani, shin Bahaushe zalla na da ‘yancin kafa ƙungiya a Najeriya? Shin a yau kuma a wannan zamani na ƙarni na 21, wane ne Bahaushe zalla kuma ta yaya za a tantance shi har ya cancanci shiga wannan mashahuriyar ƙungiya? Haka kuma, shin su wane ne shugabannin wannan ƙungiya kuma a ƙarƙashin tagomashin wa suka tafiyar da zarafofinsu, musamman ta ɓangaren kuɗaɗe da sauransu?
Wani abin lura shi ne, su waɗannan mutane, ba za ka taɓa ganin su a zahiri suna yaɗa wannan da’awa tasu ba. Sai dai suna nan sun mamaye kafafen sadarwa na zamani. Za ka gan su a musamman Facebook da sunaye iri-iri, waɗanda da ka gani, za ka fahimci cewa ba na zahiri ba ne. An ƙirƙiri sunayen ne bisa wata manufa ta musamman, wacce ba ta alheri ba.
Akwai abubuwan lura daga ayyukan waɗannan mutane a Soshalmidiya, waɗanda ke haifar da shakka a zukatan masu hankali da tsinkaye. Abubuwa kamar yadda suke amfani da sunayen bogi, yadda suke ƙoƙarin haddasa wariya da gaba tsakanin Hausawa da Fulani, yadda suke cika da fushi da zantukar tunzura jama’a, yadda suke zagi da la’antar Malaman Musulunci, matattu da waɗanda suke raye da kuma yadda suke nuna ƙyama ga ƙabilar Fulani gaba ɗaya.
Saboda a samu sauƙin karantawa tare da bibiya cikin natsuwa da tsanani da fahimta, zan riƙa gutsura wannan muƙala ƙima-kima. Da fatan za a jure biya tare da haƙuri da juriya.
_______________













