• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

‘Yan Nijeriya za su fara bin diddigin ayyukan da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa – Minista

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
November 8, 2023
in Labarai
0
Gargaɗin Amurka kan Nijeriya na tada hankulan jama’a, kuma ya na yin illa ga tattalin arzikin ƙasa – Minista

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris

13
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

‘Yan Nijeriya za su fara bin diddigin ayyukan da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa – Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kwanan nan ‘yan Nijeriya za su samu damar iya bibiya da sa ido kan ayyukan raya ƙasa waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa.

Related posts

IBB: Kai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne

IBB: Kai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne

August 17, 2026
Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

August 13, 2026

Ministan ya bayyana haka a lokacin da ya ke ganawa da editocin wasu jaridu a ranar Litinin, a Abuja.

A yayin ganawar, Idris ya ce, “Shugaban Ƙasa ya bada umarnin a yi amfani da fasahar zamani domin bai wa ‘yan Najeriya damar sa ido, bibiya da bin diddigin ayyukan raya ƙasa waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa a faɗin ƙasar nan.

Idris ya yi kira ga masu kafafen yaɗa labarai da su bayar da goyon bayan wannan tsarin, ta hanyar buga sahihan labarai da yin adalci da sauran su.

Ya ce Gwamnatin Tarayya na ɗaukar dukkan sahihan labarai da muhimmanci domin amfanar dukkan ‘yan Nijeriya.

Ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu za ta bada damar faɗar albarkacin baki ba tare da dannewa ko tauye haƙƙin kowa ba.

Ya ce: “Ku buga rahoton abin da ya tabbata, ku rabu da dukkan abin da ku ke tababar sahihancin sa, kuma kada ku kasancewa ku na buga labaran da tabbas abin da za ku buga ɗin ya faru.

“Wannan ƙasa tamu ce baki ɗaya, kuma haƙƙin dukkan ‘yan Nijeriya su taru su gina ƙasar. Kuma mun san Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ɗan gwagwarmayar dimokiraɗiyya ne da a shirye ma ya ke ya riƙa ba su bayanan duk da ku ka buƙata daga ɓangaren sa.”

Idris ya ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na nan na fasalta gagarumin aikin wayar da kan ‘yan Nijeriya da za ta yi, ta yadda za a ƙara cusa wa jama’a kishi, ƙaunar ƙasa, haɗin kai da kuma kyawawan ɗabi’u.

Previous Post

Gargaɗin Amurka kan Nijeriya na tada hankulan jama’a, kuma ya na yin illa ga tattalin arzikin ƙasa – Minista

Next Post

Taron Duniya: Minista ya sha alwashin Nijeriya za ta ɗau nauyin sabuwar makarantar UNESCO a Nijeriya

Related Posts

IBB: Kai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne
Labarai

IBB: Kai Babban Ɗan Kishin Ƙasa Ne

August 17, 2026
Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina
Labarai

Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

August 13, 2026
An Samu Sauƙin Matsalar Tsaro: Yanzu Dukkan Kasuwanninmu Suna Ci
Labarai

An Samu Sauƙin Matsalar Tsaro: Yanzu Dukkan Kasuwanninmu Suna Ci

August 12, 2026
Next Post
Taron Duniya: Minista ya sha alwashin Nijeriya za ta ɗau nauyin sabuwar makarantar UNESCO a Nijeriya

Taron Duniya: Minista ya sha alwashin Nijeriya za ta ɗau nauyin sabuwar makarantar UNESCO a Nijeriya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Illolin Yaɗa Hotuna Da Bidiyon Aika-Aikar ‘Yan Ta’addar Daji

Illolin Yaɗa Hotuna Da Bidiyon Aika-Aikar ‘Yan Ta’addar Daji

June 7, 2026
Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

INEC Ta Nesanta Kanta Daga Zargin Baddala Ƙuri’un Zaɓen Gwamnan Kogi

November 15, 2023
Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

Zaɓen gwamna: Mutum 2,318,919 za su yi zaɓe a Imo, 1,833,160 a Kogi, 1,017,613 a Bayelsa, inji INEC

October 31, 2023
Ɗan’iyan Galadiman Katsina Ya Cika Shekara 5 A Karaga

Ɗan’iyan Galadiman Katsina Ya Cika Shekara 5 A Karaga

May 29, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)
  • Professor Bello Sa’idu: The Demise of a Literary Icon
  • Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

August 24, 2026
Professor Bello Sa’idu: The Demise of a Literary Icon

Professor Bello Sa’idu: The Demise of a Literary Icon

August 23, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.