GOBARA TA TASHI A KASUWAR MADALLA
Da tsakar ranar yau Litinin, wata gobara ta tashi a Kasuwar Madalla da ke Ƙaramar Hukumar Suleja, Jihar Neja.
Gobarar, wacce ya zuwa rubuta rahoton nan, ba a tantance sanadiyyar faruwar ta ba, ta ƙona wasu sassa na shaguna da runfunan kasuwar, musamman ma sashin masu gwanjo da kuma wasu shaguna da ake ajiye makani da sauran kayan abinci irin ta.

Wakilinmu ya tattauna da wani (ya nemi a sakaya sunansa) wanda ya gane wa idonsa gobarar, ya bayyana cewa suna zaune, kawai sai suka ga wuta ta turnuƙe saman wani shago. “Kafin mu ankara, tuni ta barbazu zuwa shaguna da runfuna na kusa,” in ji shi.
Kamar yadda wakilinmu ya jiwo, mutane sun taimaka sosai wajen amfani da ruwa da sauran abin da ya sauwaƙa domin kashe wutar. Daga bisani kuma motar kwana-kwana ta zo ita ma, su ma jami’an suka yi iya nasu ƙoƙarin har aka shawo kan gobarar.

Ya zuwa yanzu dai ba a ita tantance ƙimar asarar da aka yi ba, kasancewar mafi yawan shagunan da suka ƙone, mamallakansu ba su kusa, kasancewar ba ranar cin kasuwar ba ne.













