• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, July 10, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Siyasa

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

SIYASA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 17, 2026
in Siyasa
0
Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

Jaafar ya buɗe wa 'yan Kwankwasiyya idanu

26
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya
__________
Fitaccen ɗan jarida kuma mawallafin jaridar Daily Nigerian (online), Jaafar Jaafar, ya gabatar da wani tsokaci mai ban mamaki, a shafinsa na Facebook, dangane da matakin da Jam’iyyar NDC a Jihar Kano ta ɗauka; inda ta ayyana Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, a matsayin wanda zai zama Mataimaki ga ɗan takarar Gwamna a Jihar ta Kano.

Tun da farko, Malam Jaafar ya buɗe bayanin nasa da kaushin harshe, inda ya ce: “Ɗaukar Mustapha Kwankwaso a “Deputy Governor” ba daidai ba ne. Haƙƙi ne a gare mu, mu faɗi gaskiya duk inda muka gan ta. Kujerar “Deputy Governor” ba abar wasa ba ce.

Related posts

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

July 8, 2026
Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026

“Yau in Allah ya ɗauki ran Gwamna, Deputy za a rantsar ya maye gurbinsa. Kujera ce wacce gogaggun mutane irin su B.B. Faruk, Audu Dawakintofa, Wada Abubakar, Professor Hafiz Abubakar da sauransu suka riƙe.

Jaafar ya buɗe wa ‘yan Kwankwasiyya idanu

Ɗan jaridar, wanda ya yi fice wajen bankaɗo bahallatsar ‘yan siyasa, ya ci gaba da cewa: “Amma a haƙiƙanın gaskıya ɗaukar Mustapha a matsayin “Deputy Governor” ya saɓa da duk shika-shikan Ɗarikar Kwankwasiyya. Ni a karan kaina, Mustapha yana mutunta ni kuma ko a yanzun nan da nake wannan rubutu, na ga ya kira ni a waya. Idan maslahata zan duba, ba ni da matsala da shi. Amma a kan abin da ya shafi al’umma, ina da matsala da shi.”

Da yake magana game da halayen Mustapha Kwankwaso, Jaafar ya bayyana cewa: “Ba wai ina so na aibata Mustapha ba ne amma duk wanda ya san Mustapha ya san bai cancanci wannan kujera mai girma ba. Walau a fannin Boko ko Muhammadiyya ko mu’amula, babu inda za a ce Mustapha ya kere duk zaƙakuran mutanen da suka yi shekara da shekaru suna hidimta wa tafiyar Kwankwasiyya.”

Ya ci gaba da cewa: “Ko shi kansa Oga, a duk harkokin da yake yi na sana’a, ban ga ɗaya da Mustapha ne ke kula da ita ba. Ko manajan gona bai ba shi ba amma kuma yau a ɗora shi a gwadaben da zai yi “managing” dukiya da rayukan miliyoyin al’umma?”

Daga ƙarshe dai, babban ɗan jarida Jaafar ya ƙarƙare bayaninsa da gargaɗi da kuma neman Jam’iyyar NDC da shugabanninta da su gyara lamarin, inda ya ce: “A gyara lamarin nan, kada garin neman gira a rasa ido.”

Abin tambaya a nan shi ne, ko iyayen Jam’iyyar NDC a Jihar Kano za su ɗauki shawarar Jaafar da sauran ‘yan Kwankwasiyya da suke ganin ba a yi masu daidai ba? Lokaci ne kawai zai nuna haka.

Jama’a masu karatu, shin yaya kuke ganin wannan lamari, mene ne ra’ayinku? Ku bayyana a Comment Section.
__________

Previous Post

Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

Next Post

Dr. Bukar Usman Reviews Historical Book on the Lassa Community

Related Posts

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti
Siyasa

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

July 8, 2026
Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi
Siyasa

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC
Siyasa

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

April 9, 2026
Next Post
Dr. Bukar Usman Reviews Historical Book on the Lassa Community

Dr. Bukar Usman Reviews Historical Book on the Lassa Community

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

KWANAN WATAN HIJIRIYYA A YAU LITININ

KWANAN WATAN HIJIRIYYA A YAU LITININ

February 9, 2026
KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (3)

KTSTA: HARKAR SUFURI A HANNUN GWANI (3)

August 13, 2025
KO YANZU ZA A IYA FARA KARATU A BABBAR KWALEJIN NOMA TA NABANJE – Malam Labiru Ƙafur

KO YANZU ZA A IYA FARA KARATU A BABBAR KWALEJIN NOMA TA NABANJE – Malam Labiru Ƙafur

August 5, 2025
Muhimman Ayyukan Da Shugaba Tinubu Ya Ɗora Mani – Ministan Yaɗa Labarai

Muhimman Ayyukan Da Shugaba Tinubu Ya Ɗora Mani – Ministan Yaɗa Labarai

October 19, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana
  • Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage
  • Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

July 10, 2026
Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

July 9, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.