• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Shanshani

‘Yan Arewa Na Gina Matatun Mai ‘Yan Kudu Na Gina Matatun Giya – Reno Omokri

webmaster by webmaster
May 29, 2023
in Shanshani
0
‘Yan Arewa Na Gina Matatun Mai ‘Yan Kudu Na Gina Matatun Giya – Reno Omokri
18
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

SHANSHANI mai ƙafar yawo ya leƙa gidan marubuci, ɗan siyasa kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Reno Omokri, inda ya jiwo shi yana bayyana cewa mutanen Kudancin Najeriya, musamman na yankin Kudu Maso Gabas da Kudu Maso Kudu ba su san komai ba sai sharholiya da bushasha, a yayin da takwarorinsu na Arewa da na Kudu Maso Yamma suka ƙware wajen sarrafa dukiya domin amfanin al’ummarsu.

Da yake doka misali, Reno ya ce a kwanakin baya wani hamshaƙin ɗan kasuwa daga Kudancin Najeriya ya riƙa bugun gaba da alfaharin cewa ya gina katafariyar matatar sarrafa giya a Najeriya.

Related posts

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

December 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023

“To, ina amfanin giya? Najeriya matatar sarrafa mai take buƙata ba ta giya ba. Haka fa abin yake kasancewa. A yayin da attajiran ‘yan kasuwa daga Kudu ke rige-rigen gina matatun sarrafa barasa, shi kuwa attajiri daga Arewa, Aliko Ɗangote sai ya gina katafariyar matatar man fetur da ta fi kowace girma a duniya, a kan Dala biliyan 19.” In ji Reno.

Ya gargaɗi ‘yan Kudu da cewa ba su da bakin da za su zargi Ɗangote da laifin babbake harkar kasuwanci. “Shin akwai wanda ya ɗaure hannuwan attajiranmu, ya hana su zuba jari domin gina matatun mai a ƙasar nan?” Ya ƙalubalance su.

Marubucin, wanda ya yi ƙaurin suna wajen tsokano magana, ya ƙara da cewa nan gaba kaɗan Abdulsamad Rabi’u shi ma zai gina tasa matatar a kan Dala biliyan 9.

“Mutanen Kudu su daina kukan cewa ‘yan Arewa sun danne su. Muna da dukiya amma me muke yi da ita idan ba sharholiya da bushasha ba? Za ka ga muna kashe miliyoyin kuɗi wajen bikin binne mamatanmu amma su mutanen Arewa da farin ƙyalle suke binne mamatansu.”

NI kuwa SHANSHANI, ina cewa: Ga dukkan alamu, akwai ƙanshin gaskiya a batun Omokri. Ko kuwa yaya kuka gani?

Previous Post

Ɗan’iyan Galadiman Katsina Ya Cika Shekara 5 A Karaga

Next Post

Hotunan Mako

Related Posts

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU
Shanshani

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

December 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

August 20, 2023
Next Post
Hotunan Mako

Hotunan Mako

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Burina Rubutuna Ya Zama Silar Shiriyar Al’umma – Antin Kaduna

Burina Rubutuna Ya Zama Silar Shiriyar Al’umma – Antin Kaduna

September 10, 2023
ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (7)

ƘUNGIYAR HAUSAWA ZALLA: TA INA ZA A FARA KUMA DA WACE MANUFA? (7)

June 10, 2025
ALLAH YA JI ƘAN HAUWA ƘAMSHI

ALLAH YA JI ƘAN HAUWA ƘAMSHI

October 2, 2025
Israel/Palestine Conflict: TY Buratai Foundation Calls for Permanent Ceasefire

Israel/Palestine Conflict: TY Buratai Foundation Calls for Permanent Ceasefire

November 29, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.