Al’ummar Arewa Mu Farka
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Al’ummar Arewa na cikin wani hali da ke buƙatar farkawa da tunani mai zurfi. Shekaru da dama muna fama da matsalolin tsaro, talauci, jahilci da rashin cigaba. A yayin da sauran yankuna ke ci gaba da gina tattalin arzikinsu da bunƙasa rayuwar jama’a, mu a Arewa muna ci gaba da dogaro da gwamnati da kuma dogon tattaunawa kan batutuwan da ba sa kai ga ci gaba. Wannan ya sa ake samun giɓin da ke ƙara nuna bambanci tsakanin Arewa da Kudu a fannonin ilimi, fasaha, kasuwanci da sana’o’in dogaro da kai da sauran al’amuran rayuwa masu muhimmanci.
Wani babban abin takaici, shi ne yadda mu a Arewa muka maida hankali kan gardaddami kan batutuwan addini, maimakon mu yi amfani da addinin wajen ƙarfafa haɗin kai da ƙoƙarin cigaba.
Kuma babban ma abin takaicin, ya tsaya ne inda za ka ga ana rikici kan lamarin addinin da bai da nasaba kai tsaye da rayuwar al’umma. Misali, za ka ji ana magana kan makomar al’ummar da suka gabata, ko a riƙa kutse zuwa lamarin iyayen Manzon Allah (saw) da sauransu. Wannan hali ya hana Arewa shiga sabbin hanyoyin bunƙasa rayuwa da fasahar zamani, kamar yadda sauran sassan ƙasar nan suke yi.
Idan muka duba al’ummar Kudu, za mu ga cewa sun maida hankali sosai wajen gina makarantun zamani, horar da matasa da ƙarfafa kasuwanci. Sun fahimci cewa ci gaban ƙasa ba ya zuwa da addu’a kawai, sai da aiki, fasaha, da jajircewa. Shi ya sa a yau, masana’antu, kamfanoni da cibiyoyin koyarwa da yawa suna can, alhali yawancin matasan Arewa na zaune babu sana’a, babu ilimi, babu burin samun cigaba a nan gaba.
Lallai kam lokaci ya yi da ya kamata matasa a Arewa su tashi daga barci, su daina zama cikin dogon jiran taimakon gwamnati ko ƙungiyoyi. Su fahimci cewa ba wanda zai zo daga waje ya gina musu rayuwa sai su da kansu. Su fara koyon sana’o’in hannu, su rungumi fasahar zamani, su yi amfani da intanet da dabaru wajen neman ci gaba. Duniya ta canza, kuma wanda bai tashi ba, zai ci gaba da zama a gefe yana kallon sauran suna tafiya.
Haka kuma, shugabannin Arewa, manya da ƙanana, ya kamata su daina yin siyasar raba kan al’umma, wacce ke haifar da gaba da ƙiyayya. Ya zama wajibi su daina amfani da addini, ƙabilanci da ɓangaranci wajen samun muradunsu na siyasa. Idan aka mayar da hankali wajen saka jari a ilimi, lafiya, noma, kasuwanci da tsaro, Arewa za ta dawo da martabarta. Amma idan muka ci gaba da dogaro da tunanin cewa “Allah zai yi” ba tare da mun yi ƙoƙari, mun yi aiki ba, to babu abin da zai canza.
Ya kamata malamai, mawaƙa, da ‘yan jarida su mayar da hankali wajen faɗakar da jama’a kan muhimmancin aiki da ci gaba. Kada su tsaya kan yin suka ko rikici kan finafinai da mawaƙa da ƙwallon ƙafa da sauran wasanni. Dole mu gane cewa addini da al’adu ba sa hana cigaba, sai dai suna tsara yadda za a same shi cikin tsari da mutunci. Idan muka yi watsi da wannan, Arewa za ta ci gaba da zama baya cikin al’umma, a wannan zamani na cigaba.
Wannan kira ne ga kowane ɗan Arewa, lallai ne mu farka daga dogon barcin da muke ciki. Mu daina ɓata lokaci kan batutuwan banza, mu tashi tsaye wajen gina makomarmu da ta ‘ya’yanmu. Arewa tana da albarkatu, tana da mutane masu ƙwarewa amma rashin haɗin kai da son zuciya ne suke hana ta ci gaba. Lokaci ya yi da za mu tashi, mu jajirce, mu farka, domin duniya ba ta raggo ba ce!
Jama’ar Allah, wace shawara za ku ƙara mana, domin mu gina al’ummarmu a wannan zamani na cigaba? Ku bayyana mana a Comment Section:
_______________













