An Samu Gawar Jami’in Kwastam A Ɗakin Otel Da Mata Uku A Katsina
Daga Wakilinmu
_______________
An samu gasar wani jami’in Hukumar Kwastam da ya mutu a ɗakin wani otel da ke cikin birnin Katsina. Jami’in, wanda ke da muƙamin Assistant Superintendent of Customs, an sakaya sunansa.
Kamar yadda shafin Zagazola Reports ya wallafa, an bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 15 ga Oktoba, inda jami’in ya kama ɗaki. Ma’aikatan otal ɗin ne suka samu gawarsa a ɗakin da ya kwana da misalin ƙarfe 8:30 na safe, suka kuma sanar da hukumomi nan take.
Majiyoyi sun ce an gano ƙananan ledoji da ke ƙunshe da wani gari, wanda ba a tantance mene ne ba, a cikin kwandon shara na ɗakin. Rahoton ya ƙara da cewa mata uku ne suka kasance tare da shi a otal ɗin, lokacin da abin ya faru. An bayyana sunayensu da: Khadija Ali (mai shekara 34) daga Unguwar Dutsin Amare, Katsina da A’isha Lawal (mai shekara 30) daga Ƙaramar Hukumar Ingawa da Hafsat Yusuf (mai shekara 22) daga Unguwar Birged, Kano.
An ce Khadija da A’isha ne suka kwana tare da jami’in a ɗakin, sai daga baya Hafsat ta iso ta kuma zauna a otal ɗin tare da su.
An dauki gawar marigayin zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya (FMC), Katsina, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsa, kafin a kai ta ma’ajiyar gawa domin gudanar da binciken sanadin mutuwar tasa.
An kuma bayyana cewa Hukumar Kwastam ta Najeriya ta samu rahoton lamarin, kuma ana ci gaba da bincike domin gano haƙiƙanin abin da ya jawo mutuwar jami’in._
______________












