• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, May 18, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Tunawa Da Aboki Auwal Ɗanbarno

ADABI

Muhammad Lawal Barista by Muhammad Lawal Barista
October 6, 2025
in Adabi
0
Tunawa Da Aboki Auwal Ɗanbarno

Muhammad Lawal Barista (a sama) da Marigayi Auwal Ɗanbarno

24
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Tunawa Da Aboki Auwal Ɗanbarno
Daga Muhammad Lawal Barista

Allah ya ji ƙan Auwal Ɗanbarno


                              •••••••
A lokacin da wannan bawan Allah (Auwal Ɗanbarno) yake raye, ba ma ga maciji sam, ba ma iya zama a inuwa ɗaya, a fannin ra’ayi.

Related posts

ALHAMDU LILLAH

ALHAMDU LILLAH

May 15, 2026
Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026

A mafi yawancin lokuta, duk abin da zai zo da shi, duk ingancinsa, zan bijire masa, kamar yadda shi ma, hakan yake yi a kaina, galibin lokuta. Amma fa abin da mutane ba su sani ba, ba ma haura mako guda ba mu haɗu ba. Idan har ban neme shi mun haɗu ba, to, shi zan neme ni.

Ya sha faɗa mani cewa yakan yi rubutu ya goge, ko ya yi ta gyare-gyare a kansa kafin ya sake shi, saboda gudun kar in kama shi a rubutun. Haka nan, yana haƙura da wani rubutun ma idan ya tuno ni, don ya san ba zan taɓa bari ba. Ni ma kuma haka abin yake a nawa ɓangaren. Idan kuma har ya zama dole sai ya yi rubutun, yana kira na a waya, ya ce don Allah kar in yi magana, akwai manufar da yake so ya cin ma wa a rubutun.

A iya tunanina, sau uku muka taɓa zama a inuwa ɗaya, kuma ra’ayi ɗaya a harkokin rubutu da marubuta. Na farko shi ne a 2005, yayin da aka yi taron marubuta na ƙasa a Jihar Kano, bayan tasowar wata turka-turka. Sai Kuma shekarar 2009, lokacin da na ce zan fito takarar Shugaban Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa, reshen Jihar Kano (ANA). Sai kuma a lokacin da muka yi wata haɗaka ta buga wani littafi, ni da shi da Kabiru Yusuf Fagge.

Na san wasu za su ce, to, mene ne asalin abin da ya haɗa mu, ya sa ba ma jituwa? Wannan kuwa dogon labari ne, da ba zai yiwu in kawo shi a wannan gajeren rubutu ba. A taƙaice dai, Auwalu Garba Ɗanborno, Babban Yarona (kamar yadda nake kiransa), mutumin kirki ne kuma mai damuwa da damuwar waɗanda yake tare da su.

Babu shakka, lokacin da labarin rasuwarsa ya riske ni, na yi matuƙar girgiza, don ko ba komai, na rasa abokin gwagwarmaya da fafatawa.

Ina roƙon Allah Ta’ala ya ji ƙan shi da rahama, ya haskaka kabarinsa, ya kyautata kwanciyarsa, ya yafe laifuka da kurakuransa, ya sanya aljannar Firdausi ce makomarsa. Amin-Summa-Amin!

Previous Post

Abin Da Ya Sa Muka Karrama Jami’an Tsaro A Malumfashi

Next Post

ALIYU ƘANƘARA YA ZAMA FARFESA

Related Posts

ALHAMDU LILLAH
Adabi

ALHAMDU LILLAH

May 15, 2026
Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
Adabi

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Adabi

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
Next Post
ALIYU ƘANƘARA YA ZAMA FARFESA

ALIYU ƘANƘARA YA ZAMA FARFESA

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

COMMENDATION: Essence of Loyalty to a Principal

Muhimmanci Da Tasirin Biyayya Ga Ubangida

August 25, 2025
Janar Faruk Yahaya Ya Zama Zaruman Sakkwato

Janar Faruk Yahaya Ya Zama Zaruman Sakkwato

August 15, 2023
BETARA

BETARA

February 25, 2024
TSOKACINMU NA YAU (07)

TSOKACINMU NA YAU (07)

March 7, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki
  • Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447
  • ALHAMDU LILLAH

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

May 18, 2026
Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

May 18, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.