YADDA NA ƊAUKI SHEIKH YAKUBU YAHAYA KATSINA
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Na daɗe ina bibiyar harkokin Malam Yakubu, musamman ma lokacin da nake aiki a Katsina, a tsakanin shekarun 1990. Yana daga cikin malamai mabiya mashabar Shi’a da nake gani da ƙima.
Akwai dalilai masu tarin yawa da suka sanya yake burge ni. Wasu daga cikin dalilan su ne, shi malami ne mai ILIMI, kuma da ilimin yake aiwatar da nasihohinsa da karatuttukansa. Madamar za ka saurare shi, to tabbas za ka fahimci karatunsa kuma za ka gane cewa ba kame-kame yake ba (irin wancananka).
Wani dililin da ya sa yake burge ni shi ne, yana da son zaman lafiya. A tsawon kasancewarsa shugaba a Jihar Katsina, ba a cika samun hatsaniya tsakaninsa da gwamnati ko mutanen gari ba. Wannan kuma ya samu ne saboda nagartar shugabancinsa.
Haka kuma Malam Yakubu yana da haƙuri da hangen nesa matuƙa. Yana nuna dattako a cikin lamurransa. Misali, ko a kwanakin baya da matar Zakzaky da magoya bayanta suka yi ta yi masa tijara da tozarci, bai ɗauki al’amarin da zafi ba. Ya riƙa bin abin cikin hikima.
Da a ce shi ba dattijo ba ne, lallai da ya biye wa mabiya an yi “ƁATATTA” tsakaninsa da Iyalan Sheikh Zakzaky. Amma ya jure wa cin kashin da suka yi ta yi masa. Yara sun riƙa shiga Soshalmidiya suna yi masa shaguɓe da waƙoƙin zambo, wasu ma har da zage-zage. Amma ko a jikinsa. Ya jure, saboda haƙurinsa da tsinkaye mai kyau.
Waɗannan halaye nasa nagartattu, su ne ma suka sanya, a lokacin da “MAJIYATA” ta sanar da ni cewa zai je GAISUWAR BUHARI DAURA, na amince da cewa lallai zai iya. Domin kuwa shi mutum ne mai jin ƙai da yafiya. Kuma shi ya san irin tasiri da alfanun da ke akwai ga mutumin da ya MAIDA ALHERI GA MUGUNTA. Ya san haka halayen Manzon Allah (saw) ne. Babu wanda zai zama mai yafiya, mai biyar wanda ya yi masa sharri da alheri, sai nagartaccen mutum mai koyi da Manzon Allah.
Wannan dalili ne ya sanya ko kaɗan ban yi mamaki ba, lokacin da na samu labarin cewa zai je Daura. To, amma komai sai Allah ya yarda, don haka bai samu zuwa ba. Amma tabbas na kyautata masa zato.
Malam Yakubu Yahaya Katsina – ina yi maka fatan alheri, tare da addu’ar Allah ya ƙara maka ilimi da fahimtar gaskiya.
__________
Bashir Malumfashi, Editan Mujallar Taskar Gizago (online)














Slm wallahil azem kaibakadauki mal.yaqub yahya(h)da mutunciba saboda naga bakakaunar malaminsa da iyalansa amma abintambaya yaushenekaji iyalan malam sunyima shaik yakubu wulaqanci? Allah yatadaka ranar shaida gobe qiyama dukwannan maganganun dakai nakaiwa mal.yakubu yagani ajiya kuma yafada cewar kai maqiyin harkane kuma munacigabada addua.kanku allah rusame qarya kai malam kabincika tarihi dukwani maqiyin malam zakzaky baici nasara kansaba tundaga yan tawayiyya yan zuhudu gwamnati kuma tun abacha izuwayau malam yaga bayansu barekai qaramin shedan inatausayinka amma bakinka zayajawomaka ruwan dafakanka