• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Sabuwar Kwalejin Ilimin Noma A Ƙafur/Malumfashi Za Ta Bunƙasa Ilimi a Jihar Katsina

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 19, 2025
in Babban Labari
0
A New Dawn for Agricultural and Technological Education in Malumfashi/Kafur

Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa'id Ahmad da sauran Mambobin Cibiyar Gudanarwa da aka ƙaddamar na sabuwar Kwalejin Ilimin Noma da Ƙereƙere ta Gwamnatin Tarayya, Nabanje.

86
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Sabuwar Kwalejin Ilimin Noma A Ƙafur/Malumfashi Za Ta Bunƙasa Ilimi a Jihar Katsina

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026
A Hagu: Alhaji Ibrahim Kabir Masari ne yake amsar takardar tabbatar da kafa Kwalejin Ilimin Noma da Ƙereƙere ta Gwamnatin Tarayya, Nabanje daga Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad.

 

A wani mataki mai muhimmanci na inganta ilimi da ƙerekere a yankunan Malumfashi da Ƙafur, Jihar Katsina da ma Arewacin Najeriya baki ɗaya, an ƙaddamar da Hukumar Gudanarwa ta sabuwar Kwalejin Noma da Fasaha ta Tarayya a Nabanje, da ke Ƙaramar Hukumar Ƙafur a Jihar Katsina.

Taron ƙaddamarwar, wanda aka gudanar jiya, ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ciki har da Ƙaramar Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Said Ahmad da kuma Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Siyasa da sauransu.

A jawabin da ya gabatar a wurin taron, Alhaji Kabir ya bayyana kafuwar kwalejin a matsayin “muhimmin ci gaba na tarihi, ba kawai ga Ƙafur da Malumfashi ba, har da Jihar Katsina da Najeriya gaba ɗaya.” Ya ce kwalejin za ta taimaka wajen samar da ingantaccen ilimi, haɓaka ƙereƙere ta fuskar noma da kiwo da kuma ɗora yankin kan turbar ci gaba mai ɗorewa.

Kwalejin, wacce aka kafa ta ne sakamakon haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki da kuma ƙoƙarin Majalisar Dokoki, ta samu cikakken goyon bayan Gwamnatin Tarayya. Alhaji Ibrahim Masari ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu saboda hangen nesa da goyon bayan cigaban ilimi da na ƙasa baki ɗaya. Ya kuma jinjina wa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin da kuma Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Umar Dikko Radda, waɗanda suka taka gagarumar rawa wajen tabbatar da kafuwar wannan kwaleji.

“Wannan nasara ce ta kowa da kowa — mu kiyaye ta, mu bunƙasa ta, mu kuma gina kan alƙawuranta,” in ji Masari cikin ƙarfafa gwiwa ga al’ummar da suka halarta.

Waɗanda aka naɗa a matsayin mambobin hukumar gudanarwa ta kwalejin sun haɗa da Farfesa Oluwagbemi Tai, a matsayin Shugaban Hukuma da Dokta Muktar Habib, a matsayin Shugaban Kwaleji (Provost) da Injiniya Abdussamad Umar Jibiya da Farfesa Inuwa Shehu Usman da Labiru Musa Ƙafur mni, a matsayin mambobi.

Alhaji Ibrahim Masari ya bayyana gamsuwarsa da ƙwarewar mambobin kwamitin, yana mai cewa za su jagoranci kwalejin zuwa tudun mun tsira ta fuskar bunkasa ilimi mai inganci da bunƙasa ci gaban ƙasa.

Kwalejin za ta kasance cibiyar koyarwa da bincike kan harkar noma da kiwo da fasaha, inda za a horar da matasa da ƙwararru domin bunƙasa harkokin noma da kwo a Najeriya.

Al’ummar Ƙafur da Malumfashi da kewaye sun karɓi wannan ci gaba da farin ciki, suna kallonsa a matsayin mafita ga rashin aikin yi da kuma hanyar bunƙasa rayuwar al’umma.

Ana sa ran Kwalejin Noma da Fasaha ta Tarayya, Nabanje, za ta taka muhimmiyar rawa wajen sauya tsarin tattalin arziƙi da ci gaban al’ummar Ƙafur, Malumfashi da Jihar Katsina da ma Najeriya baki ɗaya.

Previous Post

A New Dawn for Agricultural and Technological Education in Malumfashi/Kafur

Next Post

Ɗan Iyan Galadiman Katsina Emerges Chairman of Arewa Consultative Forum

Related Posts

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna
Babban Labari

Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

January 14, 2026
Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin
Babban Labari

Kishin Ilimi Ya Sa Ni Tallafa Wa Ɗalibai 110 A Malumfashi Da Ƙafur – Dokta Tukur Tingilin

January 4, 2026
Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci
Babban Labari

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

January 3, 2026
Next Post
Ɗan Iyan Galadiman Katsina Emerges Chairman of Arewa Consultative Forum

Ɗan Iyan Galadiman Katsina Emerges Chairman of Arewa Consultative Forum

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Koyaushe Talakka Zai Fita Daga Ƙuƙumi?

Koyaushe Talakka Zai Fita Daga Ƙuƙumi?

June 2, 2023
Ta’aziyyar Ɗanbarno: Daga Fasihin Mai Zane Kamal Iyantama

Ta’aziyyar Ɗanbarno: Daga Fasihin Mai Zane Kamal Iyantama

July 5, 2023
Barkwancin Ƙarshen Mako

Barkwancin Ƙarshen Mako

July 30, 2023
Go Back to the Roots, Write in African Tongues – PAWA

Go Back to the Roots, Write in African Tongues – PAWA

March 18, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.