Yadda Bikin Ƙaddamar da littafin SIRRIN MACE MUSULMA Ya Gudana A Kabo
Daga Mukhtar Yakubu

A daidai lokacin da ake ganin harkar rubutun littattafan Hausa tana samun koma baya sakamakon yadda kasuwar littafin take durƙushewa, sai ga shi ana samun wasu masu kishin Hausa da ci gaban adabin suna iya ƙoƙarin su domin ganin harkar ba ta kai ga durkushewa ba.
Fatima Aminu Alhassan Kabo tana ɗaya daga cikin mata da suka tsaya tare da jajircewa wajen rubutun littattafai a wannan lokacin. Bisa ƙoƙarin nata na samar da littafin da zai koyar tare da faɗakar da al’umma abin da ya shafi zamantakewar rayuwar aure, musamman mata a wannan lokacin; don haka ne ta yi namijin ƙoƙari wajen wallafa littafin “Sirrin Mace Musulma” domin bayar da gudummawarta ga al’umma.
A ranar Asabar, 17 ga Mayu ne dai aka yi taron ƙaddamar da littafin a Ƙofar Fadar Hakimin Kabo, da ke Karamar Hukumar Kabo a Jihar Kano.
Bikin, wanda ya samu halartar manyan baƙi kama daga ‘yan siyasa da sarakuna da malaman addini, an fara ne da taƙaitaccen bayani daga Babban Baƙo mai jawabi, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino. Ya yaba wa marubuciyar bisa ƙoƙarinta na rubuta da littafin, wanda a ganin sa; ba ƙaramin ƙoƙari ba ne.
A ta bakinsa, ” Rubutun littattafai a yanzu sai wanda ya daure kuma ya yarda sadaukarwa ne rubutun da ya yi, domin ba da gudummawarsa.”
Don haka ya yi kira ga al’umma da su daure su sayi littafin, domin amfanuwar su ga abubuwan da littafin ya ƙunsa. Haka nan ya yi kira ga ‘yan siyasar yankin na Ƙaramar Hukumar Kabo da ma na Jihar Kano baki ɗaya da su ɗauki nauyin buga littafin da yawa domin rabawa ga makarantu, don ƙaruwar su da ilimin da ke cikin littafin.
Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo, Alhaji Lawal Najumen Kano, wanda shi ne Babban Mai Ƙaddamarwa, ya nuna farin cikinsa a game da samar da wannan littafin, wanda kuma ya kasance marubuciyar ‘yar ƙaramar hukumarsa ce ta Kabo. Don haka ya ƙara jinjina a gare ta, tare da ba ta ƙwarin gwiwa don ganin ta ci gaba da rubuta da littattafai masu inganci don faɗakar da al’umma. Ya ƙaddamar da sayen kwafin littafin a kan Naira miliyan ɗaya da rabi. Yayin da Ƙaramar Hukumar Kabo ta saya a kan Naira miliyan ɗaya.













