Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin da Peter Obi ya ce ƙaramin kasafin ƙarshen 2023 ba shi da amfani
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa ƙaramin kasafin ƙarshen 2023 wanda Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sa wa hannu a ranar Laraba, ya na da muhimmanci matuƙa.
Bayanin ya biyo bayan wani kalami da ɗan takarar shugaban ƙasa na LP a zaɓen 2023, Peter Obi ya yi, inda ya ce akwai rashin tunani a kasafin, kuma bai kamata ba.
Idris ya ce kasafin ya zama wajibi a daidai wannan lokaci, domin fuskantar hanyoyin magance waɗansu matsalolin da suka shafi tattalin arziki da ake fuskanta yanzu a Nijeriya.
Minista Idris ya yi kira ga Obi cewa ya samu lokaci, ya zauna ya natsu ya yi nazarin kasafin na Naira tiriliyan 2.17 dalla-dalla, wanda ya ƙunshi: tsaro, bunƙasa fannin noma da wadata abinci, ayyuka da gidaje, ƙarin albashi da biyan alawus-alawus ga ma’aikata, bayar da rance ta ɗaliban jami’o’i da na makarantun gaba da sakandare, bada tallafi ga marasa galihu da sauran su.
Cikin wata sanarwa da Hadimin Minista a Fannin Yaɗa Labarai, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Alhamis, Minista Idris ya ce babban abin da ake buƙatar a cimma shi ne ƙarfafa tubulan da ke ɗauke da tattalin arzikin ƙasa, domin inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.
“Abubuwan da ke cikin kasafin duk kyakkyawan tunani ne da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bijiro da shi, saboda shauƙin sa na ganin ya taimaka ma’aikatun gwamnati sun fara gudanar da muhimman ayyukan raya ƙasa a cikin gaggawa, musamman maida hankali kan matsalolin tsaro, da kuma gaggauta ɗora tattalin arzikin Nijeriya kan hanyar farfaɗowa cikin sauri, bayan cire tallafin fetur da aka yi,” inji Idris.
Daga nan sai ministan ya shawarci ‘yan adawa cewa su riƙa yin nazarin alfanu da alherin duk wasu ayyukan raya ƙasa da gwamnati ta bijiro da su, kafin su kushe shi tukuna.
Ya ce yin nazarin kafin su faɗi ra’ayin su abu ne mai fa’ida, domin a ko da yaushe su na da ‘yancin bayyana ra’ayi.
Idris ya ce ba ido-rufe aka bijiro da wannan ƙaramin kasafi na Naira tiriliyan 2.17 ba, sai da aka tuntuɓi masana da sauran dukkan masu ruwa da tsaki, kuma suka tabbatar da cewa kasafin ya yi daidai da buƙatun ‘yan Nijeriya a wannan lokacin.
A ƙarshe Idris ya tabbatar wa Obi cewa a kasafin an bi ƙa’idar tantance sahihancin adadin kuɗaɗen da kowace kwangila ke buƙata, kamar yadda Shugaba Tinubu ya bijiro da tsarin bin diddigin kwangiloli da tabbatar da an kashe kuɗaɗe ta hanyoyin da suka dace.













