• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, June 15, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin da Peter Obi ya ce ƙaramin kasafin ƙarshen 2023 ba shi da amfani

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
November 10, 2023
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin da Peter Obi ya ce ƙaramin kasafin ƙarshen 2023 ba shi da amfani

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu

13
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin da Peter Obi ya ce ƙaramin kasafin ƙarshen 2023 ba shi da amfani

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa ƙaramin kasafin ƙarshen 2023 wanda Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sa wa hannu a ranar Laraba, ya na da muhimmanci matuƙa.

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026

Bayanin ya biyo bayan wani kalami da ɗan takarar shugaban ƙasa na LP a zaɓen 2023, Peter Obi ya yi, inda ya ce akwai rashin tunani a kasafin, kuma bai kamata ba.

Idris ya ce kasafin ya zama wajibi a daidai wannan lokaci, domin fuskantar hanyoyin magance waɗansu matsalolin da suka shafi tattalin arziki da ake fuskanta yanzu a Nijeriya.

Minista Idris ya yi kira ga Obi cewa ya samu lokaci, ya zauna ya natsu ya yi nazarin kasafin na Naira tiriliyan 2.17 dalla-dalla, wanda ya ƙunshi: tsaro, bunƙasa fannin noma da wadata abinci, ayyuka da gidaje, ƙarin albashi da biyan alawus-alawus ga ma’aikata, bayar da rance ta ɗaliban jami’o’i da na makarantun gaba da sakandare, bada tallafi ga marasa galihu da sauran su.

Cikin wata sanarwa da Hadimin Minista a Fannin Yaɗa Labarai, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Alhamis, Minista Idris ya ce babban abin da ake buƙatar a cimma shi ne ƙarfafa tubulan da ke ɗauke da tattalin arzikin ƙasa, domin inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

“Abubuwan da ke cikin kasafin duk kyakkyawan tunani ne da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bijiro da shi, saboda shauƙin sa na ganin ya taimaka ma’aikatun gwamnati sun fara gudanar da muhimman ayyukan raya ƙasa a cikin gaggawa, musamman maida hankali kan matsalolin tsaro, da kuma gaggauta ɗora tattalin arzikin Nijeriya kan hanyar farfaɗowa cikin sauri, bayan cire tallafin fetur da aka yi,” inji Idris.

Daga nan sai ministan ya shawarci ‘yan adawa cewa su riƙa yin nazarin alfanu da alherin duk wasu ayyukan raya ƙasa da gwamnati ta bijiro da su, kafin su kushe shi tukuna.

Ya ce yin nazarin kafin su faɗi ra’ayin su abu ne mai fa’ida, domin a ko da yaushe su na da ‘yancin bayyana ra’ayi.

Idris ya ce ba ido-rufe aka bijiro da wannan ƙaramin kasafi na Naira tiriliyan 2.17 ba, sai da aka tuntuɓi masana da sauran dukkan masu ruwa da tsaki, kuma suka tabbatar da cewa kasafin ya yi daidai da buƙatun ‘yan Nijeriya a wannan lokacin.

A ƙarshe Idris ya tabbatar wa Obi cewa a kasafin an bi ƙa’idar tantance sahihancin adadin kuɗaɗen da kowace kwangila ke buƙata, kamar yadda Shugaba Tinubu ya bijiro da tsarin bin diddigin kwangiloli da tabbatar da an kashe kuɗaɗe ta hanyoyin da suka dace.

Previous Post

Harkokin Adabi A Arewacin Najeriya: Jiya, Yau Da Gobe

Next Post

An Karrama Ɗanmadamin Yusufari Da Kambin Yabo Da Girmamawa

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
An Karrama Ɗanmadamin Yusufari Da Kambin Yabo Da Girmamawa

An Karrama Ɗanmadamin Yusufari Da Kambin Yabo Da Girmamawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

JARUMAR TIKTOK BABIYANA TA KAI ƘARAR MUSULMIN AREWA GA TINUBU DA VDM

JARUMAR TIKTOK BABIYANA TA KAI ƘARAR MUSULMIN AREWA GA TINUBU DA VDM

July 6, 2025
DISCOS or Agents of Darkness?

DISCOS or Agents of Darkness?

April 25, 2024
The Federal Capital Territory Abuja: The Past, Present and the Future

Babban Birnin Tarayya Abuja: Jiya Da Yau Da Gobe

September 19, 2023
JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

JIHAR KATSINA/MALUMFASHI MUN YI BABBAN RASHI

February 24, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Deepening Security Crisis: Buratai Calls for Emergency Measures
  • A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?
  • Inna Lillahi… We Lost Gen. Rabe

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Deepening Security Crisis: Buratai Calls for Emergency Measures

Deepening Security Crisis: Buratai Calls for Emergency Measures

June 14, 2026
A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?

A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?

June 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.