Yau Aka Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Al’ummar Jihar Katsina
~~~~~~~
An yau Talata (10-10-2023) Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya jagoranci ƙaddamar da Dakarun Tsaron Al’ummar Jihar Katsina (Katsina State Community Watch Corps.
Adadin jami’an su 1, 500 ne aka ƙaddamar, a yayin wani ƙwarya-ƙwaryan biki, a filin wasa na Muhammadu Dikko da ke, Katsina.
Bikin dai ya samu sanya albarka daga tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari da kuma Gwamnonin Jihohin Kano, Zamfara, Kebbi, Sakkwato da Yobe.
Haka kuma tare da waɗannan dakaru, an kuma ƙaddamar da Gidauniya Ta Musamman Domin Kula Da Harkar Tsaro A Jihar Katsina (Katsina State Security Intervention Trust Fund). Haka kuma an baje kolin motoci da babura masu yawa, a matsayin kayan aikin jami’an.
Wannan na zuwa ne a wani babban yunƙuri na magance matsalar tsaro da take addabar sassa daban-daban na Jihar Katsina, musamman ma dai ‘yan ta’adda da suka jima suna barazana ga al’ummar jihar.
Ana da yaƙinin cewa, wannan yunƙuri na Gwamnatin Malam Dikko zai haifar da ɗa mai ido, musamman ma ganin cewa, gwamnatin ta samar masu da kayan aiki na zamani.
~~~~~~~












