• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, April 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 5, 2023
in Babban Labari
0
MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu

Arewa Ana Kashe Mu

34
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026

~~~~~~~
Assalamu alaikum. Da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya.

Bayan gaisuwa da girmamawa, wannan saƙo ne na musamman ga Jigajigan Arewa, waɗanda ke riƙe da ragamar TSARO a Gwamnatin Mai Girma Shugaban Ƙasa Alhaji Ahmad Bola Tinubu, wato mai girma Malam Nuhu Ribadu (Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Ta Fuskar Tsaro) da Alhaji Badaru Abubakar (Ministan Tsaro) da Alhaji Bello Matawalle (Ƙaramin Ministan Tsaro).

A yau dai Arewa tana cikin matsalar tsaro mafi muni. A kullum sai an kashe al’umma. A kullum sai an sace mutane. A kullum sai an kassara mutane.

Rahotanni daga Jihar Sakkwato, ba su da daɗin ji ko kaɗan, domin kuwa ‘yan ta’adda sun kafa sansani, a kullum sai ɗaukar mutane suke, suna kashe wasu, suna amsar kuɗin fansa ga wasu. Ko a shekaranjiya, sun shiga Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, sun saci kayan abinci kuma sun yi barazana ga rayukan ɗalibai.

A Jihar Zamfara kuwa, abin ya zama sai ‘lahaula walaƙuwwata…’ domin kuwa babu safiya, rana ko daren da ‘yan ta’adda ba su sacewa, kashewa da yi wa mata fyaɗe da cin zarafi. Ko a makon jiya, sai da suka shiga Jami’ar Tarayya ta Gusau, suka sace ɗalibai mata fiye da dozin ɗaya.

A Jihar Katsina ma al’amarin ya zama gagarabadau. Ƙananan hukumomin Faskari, Ɗandume, Sabuwa, Funtuwa, Malumfashi da Ƙafur da Ƙanƙara da Dutsin-ma, kullum suna fuskantar barazanar ‘yan ta’adda. A yanzu maganar da ake Allah ne kaɗai ya san adadin mutanen da ke hannun ‘yan ta’adda.

Ko a asubahin Talatar da ta gabata, ‘yan ta’adda sun shiga gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Dutsin-ma, suka sace ɗalibai mata guda biyar.

A sanadiyyar rashin tsaro a Arewa, tattalin arziƙinmu na noma da kiwo da kasuwanci duk sun ɓalɓalce. An kassara harkar ilimi, domin kuwa ɗalibanmu maza da mata suna cikin barazana. Al’amura sun durƙushe.

Ya masu girma shugabannin tsaro, don Allah ku yi abin da ya dace, ku haɗa kan Gwamnonin Arewa da Sarakuna da Malaman Addinai da Manyan Attajirai da dukkan shugabannin Arewa domin tattauna hanyar kawo ƙarshen wannan babbar matsala. Shin haka za ku zuba ido ANA TA KASHE MU?
~
A’A – wajibi ne ku yi abin da ya dace, domin kawo mana ƙarshen wannan fitina. Ku ne idanunmu da kunnuwanmu a wannan gwamnati ta Shugaba TINUBU. Allah Ya ba ku ikon yin abin da ya dace. Amin-summa-Amin!

~~~~~~~
Daga Bashir Yahuza Malumfashi,
Babban Editan Mujallar Taskar Gizago
~~~~~~~

Previous Post

Yadda Za A Farfaɗo Da Martabar Najeriya

Next Post

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume
Babban Labari

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

April 8, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Next Post

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Tinubu Ya Ba Nuhu Ribadu Muƙami

Tinubu Ya Ba Nuhu Ribadu Muƙami

June 15, 2023
A Case For Local Police

A Case For Local Police

May 14, 2025
Sakatare Ibrahim Dasuƙi Abubakar: Al’ummar Malumfashi Ta Samu Ƙaruwa

Sakatare Ibrahim Dasuƙi Abubakar: Al’ummar Malumfashi Ta Samu Ƙaruwa

October 21, 2025
A Rayuwa Babu Abin Da Ya Kai Haƙuri

A Rayuwa Babu Abin Da Ya Kai Haƙuri

November 9, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa
  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

Malam Nasir El-Rufa’i Da Ƙalubalen Rayuwa

April 16, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.