• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, March 8, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 5, 2023
in Babban Labari
0
MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu

Arewa Ana Kashe Mu

34
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

MATSALAR TSARO: Saƙo Na Musamman Ga Jigajigan Arewa A Gwamnatin Tinubu

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

February 22, 2026

~~~~~~~
Assalamu alaikum. Da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya.

Bayan gaisuwa da girmamawa, wannan saƙo ne na musamman ga Jigajigan Arewa, waɗanda ke riƙe da ragamar TSARO a Gwamnatin Mai Girma Shugaban Ƙasa Alhaji Ahmad Bola Tinubu, wato mai girma Malam Nuhu Ribadu (Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Ta Fuskar Tsaro) da Alhaji Badaru Abubakar (Ministan Tsaro) da Alhaji Bello Matawalle (Ƙaramin Ministan Tsaro).

A yau dai Arewa tana cikin matsalar tsaro mafi muni. A kullum sai an kashe al’umma. A kullum sai an sace mutane. A kullum sai an kassara mutane.

Rahotanni daga Jihar Sakkwato, ba su da daɗin ji ko kaɗan, domin kuwa ‘yan ta’adda sun kafa sansani, a kullum sai ɗaukar mutane suke, suna kashe wasu, suna amsar kuɗin fansa ga wasu. Ko a shekaranjiya, sun shiga Jami’ar Usman Ɗanfodiyo, sun saci kayan abinci kuma sun yi barazana ga rayukan ɗalibai.

A Jihar Zamfara kuwa, abin ya zama sai ‘lahaula walaƙuwwata…’ domin kuwa babu safiya, rana ko daren da ‘yan ta’adda ba su sacewa, kashewa da yi wa mata fyaɗe da cin zarafi. Ko a makon jiya, sai da suka shiga Jami’ar Tarayya ta Gusau, suka sace ɗalibai mata fiye da dozin ɗaya.

A Jihar Katsina ma al’amarin ya zama gagarabadau. Ƙananan hukumomin Faskari, Ɗandume, Sabuwa, Funtuwa, Malumfashi da Ƙafur da Ƙanƙara da Dutsin-ma, kullum suna fuskantar barazanar ‘yan ta’adda. A yanzu maganar da ake Allah ne kaɗai ya san adadin mutanen da ke hannun ‘yan ta’adda.

Ko a asubahin Talatar da ta gabata, ‘yan ta’adda sun shiga gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Dutsin-ma, suka sace ɗalibai mata guda biyar.

A sanadiyyar rashin tsaro a Arewa, tattalin arziƙinmu na noma da kiwo da kasuwanci duk sun ɓalɓalce. An kassara harkar ilimi, domin kuwa ɗalibanmu maza da mata suna cikin barazana. Al’amura sun durƙushe.

Ya masu girma shugabannin tsaro, don Allah ku yi abin da ya dace, ku haɗa kan Gwamnonin Arewa da Sarakuna da Malaman Addinai da Manyan Attajirai da dukkan shugabannin Arewa domin tattauna hanyar kawo ƙarshen wannan babbar matsala. Shin haka za ku zuba ido ANA TA KASHE MU?
~
A’A – wajibi ne ku yi abin da ya dace, domin kawo mana ƙarshen wannan fitina. Ku ne idanunmu da kunnuwanmu a wannan gwamnati ta Shugaba TINUBU. Allah Ya ba ku ikon yin abin da ya dace. Amin-summa-Amin!

~~~~~~~
Daga Bashir Yahuza Malumfashi,
Babban Editan Mujallar Taskar Gizago
~~~~~~~

Previous Post

Yadda Za A Farfaɗo Da Martabar Najeriya

Next Post

Related Posts

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS
Babban Labari

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA
Babban Labari

Wata Mata Ta Haifi “Hatsabiban Jarirai” A Ofishin Hukumar NDLEA

February 22, 2026
Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi
Babban Labari

Musulmin Kudancin Najeriya Sun Jaddada Mubaya’a Ga Sarkin Musulmi

February 13, 2026
Next Post

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Army Chiefs Issue Strong Warning to Sahara Reporters Over Allegations

Zargin Tallafa Wa Ta’addanci: Hafsoshin Soja Sun Aika Kakkausan Gargaɗi Ga Sahara Reporters

December 8, 2025
An Yi Gangamin Addu’o’in Godiya Ga Allah A Katsina

An Yi Gangamin Addu’o’in Godiya Ga Allah A Katsina

August 1, 2023
THE MAN B. Y. M.

THE MAN B. Y. M.

June 28, 2024
Intelligence and Collaboration: Key to Defeating Insurgency in Nigeria – General Buratai

Intelligence and Collaboration: Key to Defeating Insurgency in Nigeria – General Buratai

March 5, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • RAMADAN KARIM: 19-1447
  • FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
  • RAMADAN KARIM: 18-1447

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 19-1447

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.