Jigon Ɗan Kwankwasiyya Ya Canja Sheƙa Zuwa APC
~~~~~~~
Daga Muhammadu Mustapha
Ɗan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaɓen da ya gabata, jigon ɗan Kwankwasiyya a ƙarƙashin Jam’iyyar NNPP, Haliru Dauda Jika ya canja sheƙa zuwa Jam’iyyar APC, kamar yadda jaridar Legit Hausa ta ruwaito.
A yayin bikin canja sheƙar, Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje ne ya amshi Dauda Jika a ofishin jam’iyyar ta APC a Abuja, a jiya Laraba (28-9-2023).
Da yake jawabi, Shugaban APC, Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa shawarar da Jika ya yanke ta komawa jam’iyya mai mulki tare da ƙungiyarsa a matsayin matakin da ya dace.
A jawabin nasa, Ganduje ya ce “Sanata Kwankwaso ba zai taɓa zama Shugaban Ƙasa asa ba.”
Ya ƙara da cewa, Dauda Jika ya gane cewa jam’iyyar ‘yan Kwankwasiyya ta NNPP mayaudariya ce kuma maciya amana.
A yayin bikin canjin sheƙar, Ganduje ya cire jigon Kwankwasiyyar na Jihar Bauchi jar hula ta Kwankwasiyya sannan ya maye gurbinta da hula mai ɗauke da tambarin Tinubu.
“Ya dawo jam’iyyar da ke da ci gaba da kuma mai da hankali idan muka kalli daga inda ya fito. Ya fito ne daga jam’iyyar da a baya ta kasance mai mutunci da ake ganin girmanta amma daga baya ƙungiyar Kwankwasiyya ta yi awon gaba da ita tare da gurɓata ta.
“Mun yi farin ciki da ganin cewa ainahin Jam’iyyar NNPP na gaskiya ta fara ƙwace matsayinta tare da tarwatsa ƙungiyar Kwankwasiyya da yin watsi da ita gaba ɗaya.”
~~~~~~~













