Bagizage Suleiman Idris SOA, Garkuwan Sanata Barau, ya aiko wa Gizago ra’ayinsa dangane da rushe-rushe da sabon Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya fara aiwatarwa a birnin Kano. Ga abin da yake cewa:
Gaskiyar magana a matsayina na ɗan Jihar Kano kuma ɗan adawa a wannan gwamnati, ina miƙa saƙon bangajiya da nuna goyon baya wajen wannan babban aiki da Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi jiya da dare.
Wannan aiki na rusau ya yi daidai amma a ra’ayina kuma ina da hujja wadda ina ganin in sha Allahu idan shugabanni za su ci gaba da haka, za su kai Jihar Kano mataki na ɗaya a Najeriya.
Dalilina kuwa shi ne, idan duk ya rusa wuraren da na gwamnati ne, to ka ga shi ma ba zai sayar wa wani ba nan gaba a wannan gwamnati tasa. Saboda shi ma ya san idan ya sauka, haka za ta faru da shi. Idan kuwa aka daina sayar da muhimman wuraren gwamnati, to na tabbata wata rana a jiharmu ta Kano sai ɗan siyasa ya ce da mai kuɗi zo ka sayi wannan filin na gwamnati ya ce ba zai saya ba, domin ya san wata rana wata gwamnati za ta iya rusawa.
Ka ga kuwa hakan ci gaba ne wajen gwamnati. Fili zai zauna ba wanda zai iya saye sai dai a yi wa al’ummar Kano aiki da su, kamar irin su gina makarantu, asibitoci, masallatai, maƙabartu da sauransu.
Wannan tsari ne mai kyau amma sai mutum ya yi dogon tunani. Wannan ra’ayina ne ba na kowa ba.













