Gwamnan Katsina Ya Raba Ma’aikatar Ilimi Zuwa Gida Uku
A ƙoƙarinsa na bunƙasawa da farfaɗo da darajar ili cemi a Jihar Katsina, Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya raba Ma’aikatar Ilmi ta jihar zuwa gida uku.
Wannan bayani yana ƙunshe ne a wata takardar manema labarai da ta fito daga ofishin Ibrahim Kaula Mohammed, Jami’in Watsa Labarai na Gwamnan.
Baya ga Ma’aikatar Ilimi, sauran ma’aikatun biyu da za a ƙirƙiro su ne, Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi, Ƙere-Ƙere Da Koyar Da Sana’o’in Hannu da kuma Ma’aikatar Kula Da Ilimin Firamare Da Sakandare.
Gwamna Raɗɗa ya tabbatar da haka a yayin da yake amsar baƙuncin shugabannin Jami’ar Umaru Musa ‘Yar-Adua, bisa jagorancin Shugabanta Farfesa Shehu Salihu Mohammed da suka kai wa Gwamnan ziyarar girmamawa.
Gwamnan ya ce an ɗauki wannan mataki ne da kyakkyawar niyya, da nufin inganta ilimi mai zurfi, wanda ke da matuƙar muhimmanci. Don haka ya ce, an raba ma’aikatun ne domin kawo sauƙi a gudanar da harkokin ilimi a jihar cikin inganci.
Gwamna Dikko ya yaba wa Farfesa Salihu da kuma sauran shugabannin gudanarwa, ta yadda suke tafiyar da harkokin jami’ar. Haka kuma ya yaba da kyakkyawar dangantakar da take tsakanin jami’ar da Gwamnatin Jihar Katsina.
Gwamnan ya tunatar da da cewa an kafa jami’ar ce bisa ingantaccen ginshiƙi, don haka ya buƙaci shugabannin da su yi aiki tuƙuru, domin dawo da martabar jami’ar, ta hanyar ɗaukar ƙwararrun malamai da ma’aikata haziƙai.
“Na shiga damuwa da na samu labarin cewa akwai wasu makarantu a jihar nan, inda wasu malamai ke koyar da ɗalibansu ta amfani da harshen Hausa. Wannan gaskiya abin takaici da abin kunya ne. Daga yanzu ba za mu lamunci haka ba.
“A matsayin gwamnatinmu mai kulawa, a shirye muke mu tabbatar da cewa dukkan manyan makarantunmu suna yaye ingantattun ɗalibai da za su yi gogayya da na ko’ina a faɗin duniya,” in ji Gwamna Raɗɗa.
Gwamna kuma ya jaddada albishir da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da haɗa hannu da Jami’ar Umaru Musa’ Yar-Adua, domin samar da ingantaccen ilimi abin koyi ga sauran Jihohin ƙasar nan.














Ma Sha Allah