Daga Hafiz Koza Adamu
Kyautata Wa Marayu Da Mabuƙata Alheri Ne
Farfesa Ibrahim Maqari shi ne ya assasa QAFILATUL MAHABBA. Aiki take yi ba dare ba rana. Daga cikin waɗanda ake bayyanawa a fili akwai fita da yara marayu wuraren shaƙatawa a yayin bukukuwan salla da kuma dashen itace domin amfanin al’umma.
Ana bayyana waɗannan ayyukan ne saboda a sami wasu da za su yi koyi da hakan.
A wata fira da gidan jarida, an tambayi Farfesa yaransa nawa? Sai ya ba su amsa da cewa ba ya son bayyanawa saboda kar marayun da ke ƙarƙashinsa su ji firar har su ɗauka ya bambanta su da yaransa na tsatso.














