RAHMA ABDULMAJID: Marubutan Hausa Sun Samu Wakilci A Gwamnatin Tinubu
~~~~~~~
Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya naɗa Malama Rahma Abdulmajid muƙamin Mataimakiya A Fannin Watsa Labarai

.
Rahma dai tana ɗaya daga cikin manyan marubutan Hausa kuma ta yi fice wajen wayar da kan al’umma, musamman ta yi kira domin kare martabar mata.
Jim kaɗan da samun labarin naɗin nata, Marubuta, musamman na ƙasar Hausa sun yi ta taya ta murna tare da addu’o’i na musamman, saboda a ganin su, sun samu wacce za ta wakilce su a Gwamnatin Tinubu.
Aminiyarta, Jarumar Kaduna, Zainab Muhammad Ahmad, ba ta ɓata lokaci ba, ta shiga murna. Ta shiga shafinta na Facebook ta rubuta cewa:
“A sukwane na shigo Facebook saboda murnar mun samu mulki. Alhamdu lillah, ‘yar uwa Ramu Rahma Abdulmajid ta zama PA ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tunibu. Maji daɗin Olule ta tabbata. Allah Ya sanya alheri da albarka. Allah Ya sa a fara lafiya a gama lafiya.”
Ita kuwa marubuciya Zuwaira Dauda Kolo, dogon sharhi ta yi, tare da taya murna ga Rahma. Ga abin da ta rubuta a shafin nata na Facebook:
“Tabbas bana ana yi wa marubuta gwalagwalan muƙaman da hankali bai kai wajen ba. Jiya da yau duniyar marubuta na cike da farin ciki goma da ashirin, na yadda ake ta gwangwaje su da manyan kujerun da aka san lallai sun cancanci zama wajan. A yau ma ga dai mai girma Shugaban Ƙasa ya yi abin da ya dace wajan zaɓo Shugaba Rahma Abdulmajid da ɗora ta inda ta dace.
Shugaba dai ta ko’ina ba ta taushe hannunta, don haka ku shirya ganin canji…
Ina taya ki murna Shugaba Rahama Abdulmajid. Tabbas mace mutum ce, Allah Ya ba ki ikon sauke nauyin da aka ɗora maki, Ya sa a fara lafiya, a gama lafiya.”
~~~~~~~













