Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Allahu Akbar! Allahu Akbar!! Allahu Akbar!!!
A yau ina bibiyar shafina na Facebook, kawai sai ci karo da fuskar bawan Allah, Malam Suleiman Muhammad, wanda ya rasu shekaru 10 da suka gabata.
Kafin rasuwar shi, marigayi Suleiman ƙwararren ɗan jarida ne. Ya rasu yana kan aiki da Kamfanin Media Trust Limited Abuja, mai wallafa jaridun Daily Trust da Aminiya.
Na yi aiki da marigayi Suleiman a Media Trust. Na san shi a matsayin mutum sahihi mai matuƙar haƙuri da tawali’u. Mutum ne mai amana da gaskiya.
A matsayinsa na Manajan Edita na Media Trust Limited, marigayin bai da girman kai. Yana tarairayar ma’aikatan da ke ƙarƙashinsa cikin mutunci da mutumtawa. Idan ya ga ka aikata wani abu kan kuskure, zai yi maka gyara cikin hikima, yadda za ka fahimta.
A yayin muke tuna shi, ina roƙon ‘yan uwa da abokan arziƙi da mu saka shi cikin addu’o’inmu. Ya Allah Ka jaddada masa rahama. Amin!












