Daga Bashir Yahuza Malumfashi
An Karrama Bagizage Barista Kabir Mantissa
Wasu daga rukunin tsofaffin ɗaliban Makarantar Shehu Idris Model School Kwangila Zariya sun karamma ɗaya daga cikin Gizagawan Najeriya, Barista Khalil Kabir Mantissa da Kambin Yabawa, a matsayinsa na tsohon malaminsu, wanda ya koya masu karatu shekara 15 da ta gabata.
Da yake amsar Kambin na karramawa, Barista Kabir ya ce: “Babu shakka na ji daɗin wannan karimci da kuka yi mani.”
Barista Kabir, wanda tsohon Shugaban Ƙungiyar Gizago, Reshen Jihar Kaduna ne, ya ƙara da cewa, waɗannan ɗalibai da suka karrama shi, a halin yanzu sun zama abokansa, saboda sun samu nasara a fagagen rayuwa daban-daban, kasancewar sun yi karatu mai zurfi.













