Daga Wakilinmu
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya bayyana cewa ƙarfafa dangantaka da zumunci tsakanin maƙwabtan ƙasashen Afirka ta Yamma zai bunƙasa tattalin arziƙin juna, musamman abin da ya shafi harkokin noma da kiwo.
Gwamnan ya bayyana haka ne a Larabar da ta gabata, a yayin bikin ƙaddamar da taron ƙara wa juna sani dangane da shige da fice tsakanin Jihar Jigawa da Jihar Zinder ta Jamhuriyar Nijar. Taron ya gudana ne a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa.
Gwamnan, wanda mataimakinsa, Injiniya Aminu Usman ya wakilta, ya jaddada muhimmancin wannan ƙawance tsakanin jihohin biyu, da ma ƙasashen Nijar da Najeriya, wanda ya ce zai taimaka matuƙa wajen tabbatar da zumunci mai ƙarfi da ya shafi al’adun juna, kamar kuma yadda zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙin juna ta fannin noma da kiwo.
A cewarsa, “yauƙaƙa zumunci da haɗin kai wasu hanyoyi ne sahihai na bunƙasa jituwa tsakanin mabanbantan al’ummun ƙasashen da ke maƙwabtaka da juna.”
“Babu shakka, ƙawancen zai saukaƙa harkokin kasuwanci, musamman shige da fice da kayayyaki da mutane. Nijar da Najeriya a haɗe suke a tarihi, kuma al’adunsu da yanayin rayuwarsu duk iri ɗaya ne tun taletale,” in ji gwamnan.
A yayin taron na kwana biyu, an kafa wani tsari na musamman na kula da zirga-zirgar mutane tsakanin maƙwabtan ƙasashen biyu. Haka kuma ya samu wakilci daga masu ruwa da tsaki da suka haɗa da Gwamnan Zinder da Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arziƙin Afirka ta Yamma (ECOWAS), sarakunan gargajiya, masana daga hukumomin noma da kiwo da shugabannin ƙungiyoyin manoma da makiyaya daga ƙasashen biyu.













