Hukuncin Nnamdi Kanu: Minista Bianca ta Nemi Igbo Su Guji Tada Fitina
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Minista a Hukumar Al’amuran Ƙasashen Waje, Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta yi kira ga ‘yan Najeriya, musamman al’ummar Igbo, da su kwantar da hankalinsu biyo bayan hukuncin da aka yanke wa Shugaban Ƙungiyar Rajin Kafa Ƙasar Biafra (Indigenous People of Biafra-IPOB), Nnamdi Kanu, dangane laifukan ta’addanci a Alhamis da ta gabata.
A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X a jiya Juma’a, Minista Bianca, wadda ta dawo daga birnin Zanzibar na ƙasar Tanzania, inda ta je aikin sa ido kan wata tattaunawa da ta shafi Najeriya, ta yi bayani dangane da sakamakon shari’ar da cewa “ba abin da muka zata ba ne, kuma ba abin da muka yi addu’a a kai ba amma wannan ita ce gaskiyar da muka tsinci kanmu a cikinta.”
Ta yi kira da a yi hattara, tare da gargaɗi kan duk wani abu da zai iya tayar da hankali a cikin Najeriya ko wajen ƙasar.
“Akan samu lokacin da ƙasa take buƙatar zaman lafiya. Saboda haka, ina shawartar al’ummar Igbo, da ‘yan Najeriya gaba ɗaya, cewa wannan ne lokacin. Akwai buƙatar yin hakuri da nisantar duk wata ɗabi’a da za ta tayar da hankali a wannan lokaci.
“Duk wasu matakai da za a iya ɗauka a fassara su a matsayin masu haddasa fitina, waɗanda za su iya ƙara tayar da hankalin mutanenmu na nan gida ko a ƙasashen waje, ya kamata a guje su,” in ji ta.
Odumegwu-Ojukwu ta bayyana cewa, maimakon tayar da hankali, kamata ya yi a je a tattauna, a samu haɗin kai tsakanin shugabannin Igbo, ciki har da gwamnoni, ‘yan majalisa, sarakunan gargajiya, malamai, ‘yan siyasa da shugabannin ‘yan kasuwa, domin nemo mafita tare.
Ta ce, “Hanya mafi inganci don warware wannan rikici ita ce tattaunawa. Neman zaman lafiya tsakanin Ndigbo a Najeriya bisa adalci, daidaito da mutunci wani abu ne da ke buƙatar haɗin kanmu gaba ɗaya. Kiyaye zaman lafiya da doka muhimmin abu ne domin tabbatar da tsaron ‘yan ƙasa dukkaninsu, ba tare da la’akari da ƙabila ko addini ba.”
Ta ƙara tabbatar wa ‘yan Najeriya da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa cewa, har yanzu akwai hanyoyin da za a bi don rage tashin hankali da kuma ɓacin rai da jama’a ke ciki. Ta yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a Kudu maso Gabas da su haɗu “don tattaunawa tare, cikin gaskiya, domin neman mafita a siyasance dangane da wannan lamari.”
Tun da farko dai, an yanke wa Kanu hukunci ne a ranar 20 ga Nuwamba a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa tuhume-tuhume guda bakwai na ta’addanci. Mai shari’a James Omotosho ya yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai a kan tuhuma biyar, shekaru 20 a kan tuhuma ɗaya, sannan shekaru biyar a wata tuhuma ɗaya, kuma dukkan hukuncin za su gudana a lokaci guda.
Kotun ta zaɓi hukuncin ɗaurin rai-da-rai maimakon hukuncin kisa, bisa la’akari da ƙa’idojin ƙasa da ƙasa da kuma ganin an yi adalci.
_______________













