Ni Shanshani ina zaman zama na aka iske ni da tsegumi. Wai saura kaɗan shugaban ‘yan kogo, Sheikh Abduljabbar ya samu ‘yanci.
A cikin ruɗu na waigo na ce wane ne zai ba shi rigar ‘yancin? Shin ba ka san cewa Shari’a ce ta garƙame shi ba?
Mai ba ni labarin ya ce, “ashe ba ka san bidirin da ake ciki ba? Ba ka san cewa an samu sabuwar gwamnati ba?”
Ni kuwa na ƙuta, na haɗiye wani yau da ya ɗan taru a bakina, na ce masa, ai kuwa ni na san an samu gwamnati sabuwa. Na san an rantsar da Abba Kabir Yusuf a matsayin sabon Gwamnan Jihar Kano. To me ya haɗa sabon Gwamna da batun gidan yari ko kuma sha’anin Abduljabbar?
Mutumin ya kalle ni sheƙeƙe haka, ya yi wata ‘yar dariya mai kama da yaƙe. “Haba Shanshani, ashe ba ka san Shaikh Abduljabbar cikakken mai goyon bayan gwamnatin Abba ba ne?”
Ni ma sai na yi murmushi, na ce masa “kana nufin Gwamna zai yi wa Shari’a ƙarfa-ƙarfa? Kuma shi ke nan an gaya maka shi Gwamna da ka zai yi mulkin?”
Nan da nan mutumin nan ya yi fuuu cikin fushi kamar tsohuwar kububuwa, ya harzuƙo ni da hayagaga.
“To, ka saurara ai muna nan da kai, za ka gani. Muddin muna da rai, nan da ‘yan kwanaki za ka ga Sheikh Abduljabbar a bisa ingarman doki, cikin kwalliyar ƙasaita, tare da dubban ‘yan rakiya, ya keto garin Kano daga jarun, har zuwa gidansa.”
Ni kuwa na yi shiru da bakina, na ce ba zan biye wa mutumin nan ba, don kar tsautsayi ya ɗebe shi ya ce zai b
ige ni. Kawai sai na ga mutumin ya sauko daga fushin nasa, ya ɗaga hannuwa sama kamar ƙauran da ke shirin shiga daji, ya wuce yana cewa:
“Na fito yawo gabagaɗi babu mai iya jijjiga ni!”













