• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Dokta Bukar Usman: Garkuwan Adabi Ya Cika Shekara 80

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

webmaster by webmaster
May 29, 2023
in Adabi
0
Dokta Bukar Usman: Garkuwan Adabi Ya Cika Shekara 80
7
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Idan ana maganar yi wa al’umma hidima dangane da bunƙasa ilimi da kare al’adun gargajiya a Najeriya, sunan Dokta Bukar Usman Biu dole ya buga tambura. Wannan bawan Allah ya cika shekara 80 cif a duniya. A yau za mu yi nazari da tariyar irin gudunmowar da wannan muhimmin mutum ke ba al’umma ta fuskoki da dama, musamman ma ilimi.

A ranar 10 ga watan Disamba, 2022, Doka Bukar Usman, D. Litt, M.IoD, OON ya cika shekara 80 a rayuwa. Kasancewar a irin wannan rana ta shekarar 1942 ya zo duniya, Garkuwar Adabi, kamar yadda ake masa laƙabi, bai tara mutane an yi shagulgula ba kamar yadda al’adar wasu mutane take. Mutum ne shi jajirtacce, wanda ya kai ƙololuwar ɗaukaka a aikin gwamnati kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Nazarin Al’adun Gargajiya ta Najeriya (Nigerian Folklore Society) a halin yanzu.

Related posts

Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

January 17, 2026
SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 23, 2025

Irin yadda ya ririta rayuwarsa tun daga tushe zuwa ɗaukakar matsayi, abin koyi ne ga al’ummar wannan zamani da ma masu zuwa nan gaba. Tun da farko ya fara aiki ne a matsayin ƙaramin jami’in gwamnati a Ma’aikatar Gwamnatin Tarayya, inda a shekarar 1969 ya kammala digirinsa a Jami’ar Ahmadu Bello Zariya. Hazaƙarsa da himmarsa a aiki sun ba shi damar samun ɗaukaka da ci gaba, inda ya riƙa samun ƙarin girma a lokacin da ya dace. Ta kai ga sai da ya kai muƙamin Babban Sakatare a Fadar Shugaban Ƙasa, inda ya yi ritaya daga aiki a shekarar 1999.

Al’ada ce ta manyan mutane, idan suka yi ritaya ba su ƙara yin wani aiki sai zama da hutawa a gida amma shi Dokta Bukar sai ya zaɓi ya zama mai yi wa al’umma hidima ta muhimmiyar hanyar nazari da rubuce-rubuce, wanda babu shakka ta haka yake taimakawa wajen bunƙasa ilimi da faɗakar da al’umma da adana tarihi domin al’umma mai zuwa nan gaba. Ya kasance yana amfani da dukiyarsa wajen ɗaukar nauyin nazari da binciken ilimi, sannan yakan wallafa muhimman littattafai a fagagen ilimi daban-daban, musamman ma adabi da sauransu. Kuma mafi yawa daga littattafan da yake samarwa ta hanyar Gidauniyar Bukar Usman, kyauta yake raba su ga al’umma da makarantu da cibiyoyin ilimi na sassan ƙasar nan, har ma da ƙasashen waje.

A lokacin da ya yi ritaya a shekarar 1999, Dokta Bukar yana da shekara 57 a duniya. Kafin sannan, babu wanda ya san shi da harkar rubuce-rubuce, idan ba rubuta bayanan aiki a fayil-fayil na ofis ba. Sai ga shi saboda himmarsa, cikin shekara 20 ya zama wani mashahurin marubuci, wanda sautinsa ke ruri a duniyar rubutu a fagen adabi, ilimin gudanarwa, siyasa da sauran fagage masu muhimmanci a rayuwa.

Kamar yadda ya bayyana a ɗaya daga cikin littattafansa mai suna My Literary Journey, Dokta Bukar ya fayyace yadda aka yi ma ya fara harkar rubutu, domin kuwa ya ce tun da farko ba a haife shi da jinin marubuta ba.

“A batun gaskiya, lokacin da na zaɓi in fara rubuce-rubuce bayan na yi ritaya daga aikin gwamnati, ban taɓa tsammanin zan iya ɗorewa ba. Na rubuta littafin tarihin rayuwata cikin shekarar1992, inda na kammala aka wallafa shi a shekarar 2006. Amma sauran rubuce-rubucen ƙirƙira da na adabi da sauran fagage, na fara su ne daga bisani,” inji shi.

A matsayinsa wanda ya yi wa harkar rubutu shigar sojan Badakkare, ya aminta da cewa ta hanyar adabi za a iya yi wa al’umma hidima. Babu shakka ya samu gogewa da ƙwarewa wajen sanin inda ke wa al’umma ciwo. Don haka ya san wane maudu’i ya kamata ya yi rubutu a kansa. Tun da farko bai samu horarwa a fagen rubutun ƙirƙira da adabi ba amma saboda himmarsa, sai ga shi har ya fi mai kora shafawa, ma’ana “har ya gagari ’ya’yan gado,” kamar yadda marigayi Mamman Shata Katsina ya faɗa a waƙarsa ta Bakandamiya. Ma’ana sai ga shi ya zama kamar ruwan dare gama duniya a fagen wallafa, domin kuwa ko’ina za ka ga littattafansa kuma za ka ga masana na nazari da bitar su a jami’o’i da kwalejojin ilimi.

Kamar yadda shi da kansa ya bayyana, a zamanin da yake ɗalibi bai samu damar karanta littattafan ƙirƙira ba, domin kuwa a lokacin babu su da yawa. Amma duk da haka ya kasance mutum mai ƙwazon karance-karance, wanda haka ya ba shi damar samun sha’awar yin rubutu. “Ban samu tagomashin horo a fagen rubutu ba amma na kasance mai ƙwazon karance-karance matuƙa. Idan aka ce kai mai yawan karatu ne, za ka iya koyon wata hikima da fasaha koda ba a horar da kai a aji ba.” Ya ce haka kuma a duk abin da ya rubuta yakan ba ƙwararrun masana su duba domin gyare-gyare da shawarwari, shi ya sanya ayyukansa suke fitowa da nagarta sosai.

“Haƙiƙa na samu ilimin cewa a duk lokacin da mutum ya sanya kansa a harkar rubutu, zai fuskanci ƙalubale daban-daban na musamman da suka shafi ƙirƙira, nazari bincike da kuma wallafa. Mutum zai kasance cikin aiki na tsawon lokaci a kan daftarin da ya rubuta,” inji Bukar, a yayin da yake bayyana faɗi-tashinsa a harkar wallafa.

Idan muka waiga baya daga lokacin da ya faro rubuce-rubuce, za mu iya cewa ya yi nasarar murƙushe dukkan ƙalubalen da ya riƙa fuskanta a wannan fage da ya saka kansa.

Littafinsa na farko shi ne Voices in a Choir, sai kuma Hatching Hopes (Cikar Buri), wanda na tarihin rayuwarsa ne, ya fara rubuta shi a shekarar 1992, aka wallafa shi a 2006.

Yakan yi rubutu ne a harsunan Ingilishi da Hausa. Babban aikinsa a harkar Adabin Hausa, shi ne babban kundin Taskar Tatsuniyoyi, wanda ke ƙunshe da shafuka 652. A Ingilishi kuwa, ya samar da littattafan tatsuniyoyi daban-daban, wadanda suka hada da The Bride Without Scars and Other Stories da The Stick of Fortune da kuma Girls in Search of Husbands (waɗanda ke ƙunshe da tatsuniyoyi 26). Ya yi aiki sosai wajen zaƙulo tatsuniyoyi masu daɗi da jan hankali, masu koya darussa ga musamman yara da ma al’umma baki ɗaya.

Ya zama wajibi ga al’umma su miƙa godiya ga mawallafi Duve Nakolisa, wanda shi ne mutum na farko a shekarar 2005 da ya ja ra’ayin Dokta Bukar kuma ya ƙarfafa masa gwiwa da cewa ya kamata ya jaraba hannunsa a rubuce-rubucen da suka shafi ƙirƙira da adabi. Ya ankara da himmar marubucin ne, bayan wallafa littafinsa mai taken Voices in a Choir. Tun daga lokacin kuwa ya tunkari wannan harka, inda ya zuwa yanzu ya samar da littattafai daban-daban fiye da 40 a wannan fage. Haka kuma ya ɗauki nauyin nazari da tattara tatsuniyoyin al’ummun sassa daban-daban na Najeriya da suka haɗa da na ƙasar Yarabawa da Ibo da na Tibi da sauransu.

Babu shakka Bukar Usman ya cika mutum mai kishin ƙasa da al’ummarsa, wanda ke sanya darasi ga matasa da ma dattijai, cewa yawan shekaru ba za su iya hana mutum yi wa ƙasarsa da al’ummarsa hidima ba.

A yayin da ya cika shekara 80 a duniya, muna roƙon Allah Ya ƙara masa lafiya da yawan shekaru tare da azamar ci gaba da yi wa al’umma hidima.

Next Post

Rigakafi Ne Babban Jagoran Yaƙi Da Sankarar Mahaifa – Janar Buratai

Related Posts

Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a
Adabi

Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

January 17, 2026
SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)
Adabi

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 23, 2025
Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine
Adabi

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

December 6, 2025
Next Post
Rigakafi Ne Babban Jagoran Yaƙi Da Sankarar Mahaifa – Janar Buratai

Rigakafi Ne Babban Jagoran Yaƙi Da Sankarar Mahaifa - Janar Buratai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

TARON JIGAJIGAN KATSINA ALHERI NE

TARON JIGAJIGAN KATSINA ALHERI NE

September 16, 2025
SHARI’AR MUSULUNCI: Bayan Yaƙi Da Baɗala, A Yaƙi Ɓarayin Gwamnati, Hanci Da Rashawa

SHARI’AR MUSULUNCI: Bayan Yaƙi Da Baɗala, A Yaƙi Ɓarayin Gwamnati, Hanci Da Rashawa

November 3, 2023
Kasafin 2024 Ya Fitfita Jaddada Ajandar Sassaita Nijeriya – Idris

Kasafin 2024 Ya Fifita Jaddada Ajandar Sassaita Nijeriya – Idris

December 4, 2023
GENERAL BURATAI PAYS HOMAGE TO GENERAL BUHARI

GENERAL BURATAI PAYS HOMAGE TO GENERAL BUHARI

March 9, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.