Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Jihar Katsina Na Fuskantar Barazanar Ambaliya A Daminar Bana

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗi da cewa a daminar bana, wasu jihohi, har da Katsina za su fuskanci annobar ambaliyar ruwa, musamman a cewar ta saboda za a samu kwazarin ruwan sama mai yawa a daminar ta bana.
Kamar yadda hukumar ta sanar, ta ce a hasashenta, jihohi 14 da garuruwa 31 ne za su iya samun ruwan sama kamar da bakin ƙwarya. Hakan zai iya haifar da ambaliya daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli, a cewar gargaɗin.
Kamar yadda sanarwar ta gabata, a Jihar Katsina, yankunan Katsina, Jibia, Kaita da Bindawa ne ake hasashen samun ambaliyar a bana.
Sauran jihohin da hukumar ta zayyana, waɗanda suke fuskantar bazaranar ambaliyar a bana, sun haɗa da Jihar Filato, a yankunan Langtang da Shendam. Sai Kano, yankunan Sumaila da Tudun Wada. A Jihar Sakkwato kuwa, akwai yankunan Shagari, Goronyo da Silame. A yayin da Jihar Delta, yankin Okwe ne abin zai shafa.
A Jihar Kaduna kuwa, garin Kachiya ne ke kan gaɓa. A yayin da a Jihar Akwa Ibom aka ambata yankin Upenekang.
Sauran jihohin sun haɗa da Adamawa (Mubi, Demsa, Song, Mayo-Belwa, Jimeta da Yola). Jihar Kebbi (Wara, Yelwa da Gwandu). Jihar Zamfara (Shinkafi da Gumi). Jihar Borno kuwa, yankin Briyel ne ake hasashen zai samu ambaliya.
A Jihar Jigawa, yankin Gwaram ne aka bayyana, a yayin da Jihar Kwara aka ambata yankin Jebba. A Jihar Neja, akwai yankunan Mashegu da Kontagora.
A Jihar Katsina dai, rahotanni sun bayyana cewa Gwamnatin Jihar tana shirin ɗaukar matakan da suka dace, domin tunkarar al’amarin. Ko a makon da ya gabata, Shugaban Hukumar Kula Da Muhalli Ta Jihar Katsina (SEPA) Alhaji Muhammad Kabir Usman sai da ya jagoranci ma’aikata, inda suka yashe magudanan ruwa da kwashe bola da ta toshe su.













