Daga Wakilinmu
Gamayyar Ƙungiyoyin Tsofaffin Ɗaliban Jihar Katsina sun yi kira ga Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa da ya ajiye mazaunin Jami’ar Nazarin Kimiyyar Lafiya a garin Malumfashi, Shiyyar Sanatan Kudancin Katsina.
Da yake magana a madadin ƙungiyar, ɗaya daga cikin shugabanninta, Badamasi Haiba ya ce, idan aka yi duban nazari, garin Malumfashi yana tsakiyar ƙananan hukumomi 11 da ke cikin Shiyyar Sanatan Kudancin Katsina, don haka nan ya kamata a ajiye mazauninta domin amfanin kowa cikin sauƙi.
Ya ƙara da cewa kuma ajiye jami’ar a Malumfashi shi ne daidai da adalci, domin hakan zai sauƙaƙa wa ɗaukacin ɗaliban da suka fito daga kowane lungu na shiyyar.
“Idan aka lura, sauran ƙananan hukumomi da ke Kudu Maso Kudancin shiyyar, suna maƙwabtaka da Jami’ar Ahmadu Bello da kuma Asibitin Koyarwa na ABU da ke Shika, ga kuma Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a (SBRS) da ke Funtuwa. Don haka Malumfashi ne garin da ya fi cancanta a ajiye wannan sabuwar jami’a da ake son kafawa,” in ji Badamasi.
Ya ce kuma hakan zai taimaka wa ƙananan hukumomin yankin Karaɗuwa da ma na maƙwabtansu na Jihar Kano.
“Malumfashi a matsayinsa na Hedkwatar Masarautar Katsina a shiyyar, yana dukkan gine-ginen da ake buƙata da sauran abubuwan rayuwa domin riƙe jami’ar, kuma hakan zai sauƙaƙa wa Gwamnatin Tarayya kashe kuɗi yayin kafa mazauninta,” a cewarsa.
Badamasi ya tunatar da Gwamna Raɗɗa cewa an haramta wa Shiyyar Sanatan Kudancin Katsina samun wata babbar makaranta mai darajar ba da digiri ko wata cibiyar ilimi babba, kasancewar duk an tara manyan makarantun, an kafa su a Tsakiya da Arewacin Katsina.
“Ya mai girma Gwamna, lokaci ya yi da za ka karya wannan ƙwarin, ka rubuta sunanka da ruwan gwal, ta hanyar amincewa da kafa Jami’ar Nazarin Kimiyyar Lafiya ta Gwamnatin Tarayya a Malumfashi, a Shiyyar Sanatan Kudancin Katsina, kasancewar yanki ne mai yawan al’umma, wanda ya fi kowane yankin yawan ƙuri’u a Jihar Katsina.” Kamar yadda Badamasi ya jaddada.













