Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Fitaccen ɗan jarida kuma mawallafin Jaridar Daily Nigerian ta intanet, Malam Ja’afar Ja’afar ya nuna matuƙar ɓacin rai da yadda Gwamnatin Jihar Kano a ƙarƙashin shugabancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta rusa ƙayataccen shataletalen nan mai hasumiyar algaita da ke kusa da Gidan Gwamnatin Jihar Kano.
Da yake sukar rusau ɗin da kakkausar murya a shafinsa na Facebook, ɗan jaridar ya ce: “Wajibi ne dukkanmu mu yi Allah-wadai da wannan mataki marar dacewa, na rusa wannan ƙayataccen wurin tarihi, wanda matashiyar mai zayyana ta zama domin adana tarihin Jihar Kano da ta shekara 50 da ƙirƙirowa.”
Ja’afar ya ce shi ba ya ƙyamar rushe-rushen da sabon Gwamnan na Jihar Kano yake yi, musamman wuraren al’umma da aka cefar ba bisa ƙa’ida ba.
“Ina goyon bayan rusa gine-ginen da aka yi a harabobin makarantu da asibitoci da masallatai ba bisa ƙa’ida ba. Amma ba na goyon bayan rusa muhimman gine-gine da za su amfani al’umma, kawai saboda Ganduje ne ya gina su. Ni dai ba na tsarin siyasar Ganduje amma ina son wasu ayyukansa da ya gudanar a matsayinsa na Gwamna.” In ji Ja’afar.
Shi dai Ja’afar a can baya sun yi ta sa-toka-sa-katsi da tsohon Gwamna Ganduje, a lokacin da ya kwarmata wani bidiyo, wanda ya fallasa shi, inda aka nuno shi yana cusa bandir-bandir ɗin Daloli a aljifan babbar riga; Kuɗin da aka yi zargin na cin hanci ne.














