Yakubu Muhammad Rigasa
Idan akwai wanda ke shan guduma daga ɓangarori mabanbanta, to Mallam Nasir El-Rufai ne. Kowa da irin kallon da ya ke masa.
‘Yan Kudancin Kaduna da Kudancin Najeriya na mai kallon mai tsattsauran ra’ayin addinin Musulunci saboda shi ya soma assasa mulkin Muslim-Muslim a jihar Kaduna.
Kwatsam! Kuma sai ga shi wasu ‘yan uwanshi Musulmi daga jiharshi ta Kadunan na masa kallon wanda ya yi yunƙurin rusa Musuluncin ma gaba ɗaya a lokacin da yake mulki.
Duk waɗannan ɓangarori biyu idan ka tambaye su, za ka ji babu wanda ke da wata ƙwaƙƙwarar hujja a kan abin da yake jinginawa Mallam Nasir illa dai wane-ya-ji-ga-wane.
Ta yaya mutum zai zama mai kishin addini sannan kuma mai son rusa wannan addinin dai, duka a lokaci guda? Dole ya zama ko dai duka biyun ba gaskiya su ka faɗa ba, ko kuma aƙalla ɗaya daga cikin su abin da ya ke iƙirarin ba haka ba ne.
Ni kuwa irin kallon da nake masa shi ne, mutum ne wanda ke dagewa wajen cimma duk wata manufa da yakewa kallon alheri ce ga al’umma, to fa zai sanya ta a gaba ko da kuwa zai saɓa ma waɗansu akan hanyar shi ta kai wa ga cimma wannan burin. Sannan kuma abu ɗaya dai da na tabbatar babu wanda ya isa ya musa shi ne, Mallam ya yi aikin da ba a sami wani gwamna kafin shi da ya yi wa Jihar Kaduna irin wannan aikin ba.
Kai wane irin kallo ka ke wa Mallam Nasir El-Rufai?
—
Malam Yakubu Rigasa, mai sharhi ne kan al’amuran yau da kullum!












