A kwanakin baya ne membobin ƙungiyar sada zumunta da taimakon juna ta GIZAGON NAJERIYA, a ƙarƙashin jagorancin shugabanta na ƙasa, Malam Muhammad Kabir Adam Gombe ta ziyarci ɗaya daga membobinta da ke fama da rashin lafiya, inda ta ƙaddamar da gangamin addu’a, domin Allah Ya ba shi lafiya.
Majinyacin, Malam Abdullahi Alkotonawi, wanda ke fama da lalurar hawan jini, ya samu ziyartar Gizagawan ne a gidansa da ke Unguwar Ja’en, Ƙaramar Hukumar Gwale, Jihar Kano a ranar Lahadi (14-05-2023).
“Isar ayarin Gizagawan ke da wuya sai majinyanci Malam Abdullahi ya fashe da kuka saboda shauƙi da jin daɗin ganin ‘yan uwa. Daga nan sauran ‘yan uwa Gizagawa su ma suka fara zubar da hawaye.” Inji Shugaba Muhammad Kabir.
Daga nan aka shiga ruwan addu’o’i kuma daga ƙarshe ƙungiyar ta miƙa masa tallafin Naira 128,000, da ɗaukacin Gizagawa suka tattara domin rage masa ɗawainiyar magani.
Majinyacin, wanda mutum ne mai ƙoƙarin zumunci, ya yi godiya sosai da wannan kulawa, haka shi ma ƙanensa, Malam Yahaya, inda suka yi addu’ar Allah Ya bar zumunci.
Haka kuma ayarin na Gizagawa ya kai wata ziyarar ta dubiya ga Ma’ajin Ƙungiyar Gizago na ƙasa, Malam Kabiru Ghali Abban Saudat, wanda shi ma ya sha jinya kwanakin baya.
Daga ƙarshe shugaban na Gizagawan Najeriya ya rufe ziyarar da cewa, “ina miƙa godiya ga waɗanda suka taimaka da lokacinsu, kuɗinsu, addu’o’i da jikinsu har wannan tallafi ya kammala. Allah Ya saka kowa da alheri.”













