Matasa Masu Fusata Sun Ƙone Ofishin ’Yan Sanda
Daga Wakilinmu
__________
Wasu fusatattun matasa sun ƙone Ofishin ’Yan Sanda na Isan da ke Ƙaramar Hukumar Oye a Jihar Ekiti.
Matasan, waɗanda suke zanga-zangar nuna rashin amincewa da zargin cewa ’yan sanda sun harbe wani matashi, sun sha alwashin ci gaba da gudanar da zanga-zangar har sai an yi adalci.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, wani bidiyo ne da aka samu, wanda ke nuna wani matashi kwance cikin jini ya bazu sosai a kafafen sada zumunta, musamman a shafin X, shi ne ya harzuƙa matasan.

Wani mai amfani da shafin X mai suna Stephen Ayeni ya ce wanda lamarin ya rutsa da shi, ya je filin ƙwallon ƙafa ne domin kallon wasa lokacin da abin ya faru.
Cikin fushi da wannan lamari, an ce matasa masu zanga-zangar sun mamaye ofishin ’yan sandan tare da banka masa wuta.
Wani jami’in ɗan sanda, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:00 na yamma lokacin da wasu mahara suka kai farmaki kan ofishin ’yan sandan.
A cewarsa, ɗaya daga cikin jami’an da suka jikkata, yana cikin mawuyacin hali kuma yana karɓar magani a wani asibiti.
Jami’in ya kuma bayyana cewa an lalata motoci da dama a harin, ciki har da wata bas da jami’an ’yan sanda suka yo hayarta daga Abuja.
Ya ƙara da cewa jami’an Rundunar ’Yan Sandan MOPOL, waɗanda aka sanar da harin yayin da suke kan hanyarsu daga Oye zuwa Isan, sun fafata da masu zanga-zangar, tare da hana su karɓe ikon garin.
Jami’in ya bayyana cewa wasu jami’an da ke bakin aiki sun tsere lokacin harin amma ya ce jami’an tsaro sun sake dawo da iko a yankin tare da maido da zaman lafiya.
An ga mummunar ɓarna a ofishin ’yan sandan, inda motoci biyu suka ƙone a cikin harabar ofishin. Haka kuma, wutar da suka kunna, ta lalata janareta, tagogi, ƙofofi da kuma rufin ginin. A wajen harabar ofishin kuma, an ga wasu motoci uku da suka ƙone ƙurmus.
Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ekiti ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.












