• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, May 19, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

BABBAN LABARI

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
May 13, 2026
in Babban Labari
0
Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

Hoton AI: Samfurin yadda aka kama wacce ake zargi

21
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Ta Banka Wa Mijinta, Kishiyarta Da Yara Wuta A Kano

Daga Wakilnmu

Related posts

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026
Yan ta’addan Daji Kafirai Ne  – Sarkin Musulmi

Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi

May 8, 2026
Hoton AI: Samfurin yadda aka kama wacce ake zargi

 

___________

Ana zargin wata mata mai suna Maryam Muhammad da laifin zuba wa mijinta da kishiyarta da yara biyu fetur, sannan ta banka musu wuta a unguwar Hotoro da ke cikin birnin Kano.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, kishiyar tata mai suna Firdausi Musa, mai shekaru 28 tare da ’ya’yanta ƙanana biyu sun samu munanan ƙonewa a sassan jikinsu.

Lamarin, wanda ya faru a daren jiya Litinin a yankin Mai Allo da ke Unguwar Hotoro, ya jefa mazauna yankin cikin firgici, yayin da ake tsare da wadda ake zargin a ofishin ’yan sanda na Mariri.

An bayyana sunayen yaran da suka jikkata da Khadija Ya’u mai shekaru 7 da kuma Isma’il Ya’u mai shekaru 3. Ana kula da lafiyarsu tare da mahaifiyarsu a Asibitin Ƙashi na Ƙasa da ke Dala da kuma Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano.

Mijinsu, Malam Saminu, wanda rahotanni suka ce shi ma ya samu ƙonewa yayin ƙoƙarin ceto su daga wutar, shi ma yana karɓar magani.

Da yake zantawa da jaridar Daily Trust, ƙanin Firdausi mai suna Buhari Musa Sa’ad, ya ce sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3 na dare, cewa an banka wa ’yar uwarsa da mijinta da yaran biyu wuta daga kishiyarta.

A cewarsa, Firdausi ba ta yi ko makonni biyu ba da komawa gidan aurenta kafin wannan lamari ya faru.

“Firdausi tana da kusan shekaru 28. Yaran da suka ƙone kuwa su ne waɗanda ta zo da su daga aurenta na baya,” in ji shi.

Wata ’yar uwa ga Firdausi mai suna Rukayya ta kuma shaida wa Daily Trust cewa tun kafin harin, Firdausi ta yi ta ƙorafin cewa kishiyarta tana yi mata barazana da tsangwama.

“Mun kasance a kwance a nan, lokacin da aka kawo ta kuma ita da kanta ta gaya mana cewa kishiyarta ce ta zuba mata fetur sannan ta kunna ashana,” in ji ta.

Rukayya ta bayyana cewa tun da farko a ranar, Firdausi ta bar gidan saboda yawaitar barazanar da ake yi mata amma daga baya ta koma, bayan mijinta ya shiga tsakani.

Ƙoƙarin jin ta bakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano bai yi nasara ba kafin kammala haɗa wannan rahoto.

________

Previous Post

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (12)

Next Post

ALHAMDU LILLAH

Related Posts

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi
Babban Labari

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026
Yan ta’addan Daji Kafirai Ne  – Sarkin Musulmi
Babban Labari

Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi

May 8, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Next Post
ALHAMDU LILLAH

ALHAMDU LILLAH

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

MAGAJI GALADIMA: Yau Ne Maulidin Magayaƙin Kano

MAGAJI GALADIMA: Yau Ne Maulidin Magayaƙin Kano

September 29, 2023
Matsalar Tsaro A Najeriya: Madalla Da Majalisar Dokokin Amurka

Matsalar Tsaro A Najeriya: Madalla Da Majalisar Dokokin Amurka

November 26, 2025
MALUMFASHI: MUN YI RASHIN ABOKI KUMA ƊAN UWA

MALUMFASHI: MUN YI RASHIN ABOKI KUMA ƊAN UWA

July 19, 2024
Gwamnan Katsina Ya Raba Ma’aikatar Ilimi Zuwa Gida Uku

Gov. Raɗɗa Sponsors 40 Katsina Indigenes to Study Medicine Abroad

October 6, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki
  • Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447
  • ALHAMDU LILLAH

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

Turning Point Against Terror: The Fall of Abu-Bilal Al-Minuki

May 18, 2026
Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

Barkanmu Da Shiga Watan Dhul-Hijjah 1447

May 18, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.