Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Jamila Tangaza!
“Jamila Tangaza?” Wataƙila tambayar da za ku yi ke nan, kasancewar lallai kun san sunan nan sarai amma daga baya kuka ji shiru, kamar malam ya ci shirwa. To, bari in ƙara maimaita maku sunan: Jamila Tangaza!
Babu shakka na san yanzu kun tuna da wannan sunan, domin kuwa ba zai taɓa ɓuya ba, komai tsawon zamani. Hajiya Jamila dai shahararra kuma ƙwararriyar ‘yar jarida ce, wacce ta kafa suna a aikin jarida a duk faɗin duniyar Hausa.
Ita ce ‘yar jarida mace ta farko da ta fara zama Shugaba a Sashen Hausa na Gidan Rediyon BBC kuma ta kafa babban tarihin da ya karaɗe sassan rayuwa da suka shafi, siyasa, tattalin arziki, rayuwar yau da kullum da kuma adabi. Ta gabatar da shiryen-shiryen rediyo masu ilimantarwa, faɗakarwa da gamsarwa, waɗanda suka yi tashe kuma suka samu amsuwa daga ɗinbin al’umma.
Babu aune, sai mutane suka daina jin ɗuriyarta, ta ɓace ko sama ko ƙasa. Hatta a soshalmediya, an daina ganin gilmanyarta. Wasu ma har sun fara tababar ko ta rasu ne? Amma ina, da sauran aiki…
Kamar daga sama, sai ga sanarwa daga shafinta na Facebook, inda ta bayyana ɗauke da babban albishir mai sanyaya rai ga masoyanta da ma al’umma gaba ɗaya, musamman ma masu son ilimi da ilimantarwa.
Ga abin da ta sanar, a shafin nata: “Assalamu alaikum wa rahmatullah. Bayan shekaru masu yawa, ga shi Allah ya ba ni ikon komowa filin sada zumunta na Facebook.”
Ta ce: “Mutane da yawa suna ta tambaya, cewa shekaru da yawa ba sa ji na. Ko me ya sa?
“A yunƙurina na bayyana abin da ya faru da ni bayan na ajiye aikin BBC, na koma Nigeria, na rubuta littafi mai suna: “REFUSAL: POWER, INTEGRITY, THE COST OF CONSCIENCE.”
Hajiya Jamila ta bayyana cewa wannan littafi ya ƙunshi tarihin rayuwarta. Ta yi bayani dalla-dalla kan zarge-zarge da yunƙurin ɓata suna a wancen lokaci. Ta kuma yi bayani kan yadda ta tsallake wannan ƙalubalen, bisa taimakon Allah da addu’o’in ɗinbin al’umma, musamman ma masoyanta.
Ta ci gaba da bayyana cewa a cikin littafin, ta bayyana darrusan da ta koya, musamman a ɓangaren shugabanci da abin da kan biyo bayan samun ɗaukaka, musamman ma a ƙasar Afirka, kamar Nigeria.
Tangaza ta ce har yanzu littafin yana maɗaba’a yana shan ƙwankwasa da ‘yan gyare-gyare. Sai dai ta yi wa al’umma albishir da cewa, in sha Allahu, da zarar an kammala aikin buga shi kuma ya fito, za ta sanar wa al’umma.
Game da dawowarta fagen soshalmidiya kuwa, Hajiya Jamila ta ja hankalin al’umma tare da tunatarwa. Ta ce, “a wannan lokacin da ƙasa da duniya suka kacame da matsaloli, wajibi ne mu haɗa kai domin mu taimaki kanmu. Ina rokonku da sunan Allah (swt), da mu yi mu’ala ta girmama juna, ba tare da ɓatanci, raini, ko cin zarafin kowa ba.”
Haka kuma, Hajiya Jamila ta yi togacciya da ƙa’idojin da Shari’a da Doka suka tanada, dangane da musharaƙa da juna a soshalmidiya, inda ta ce: “Kada ku manta cewa, a Nigeria, Sashe na 24 na Dokar Cybercrimes (Prohibition, Prevention, etc.) Act, 2015, wacce aka yi wa gyara a shekara ta 2024, ta haramta wasu nau’o’in aikawa ko watsa saƙonnin cin mutunci, ɓatanci, barazana, ko tsoratarwa ta hanyar kwamfuta ko hanyoyin sadarwa (wanda ya haɗa da kafofin sada zumunci, e-mail, SMS da sauransu). Yin haka na kai wa ga ɗaukar matakin shari’a, domin bin kadi.”
Da take ƙarƙare bayaninta, shahararriyar ‘yar jaridar ta ce: “A ƙarshe, ina roƙon Allah ya taimake mu, ya ƙara sutura, ya kare mu, ya ƙara mana da ƙasarmu albarka, amin. Ina godiya ta musamman ga dukkanin masoyana da ƙanina Zaidu Bala da ƙungiyoyi daban-daban da muka shafe shekaru muna mu’amala. Na gode. Allah ya saka da alheri.
__________













