• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Wednesday, April 15, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Babban Labari

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

BABBAN LABARI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
April 8, 2026
in Babban Labari
0
Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Sanata Mohammed Ali Ndume

10
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Yadda Za A Magance Matsalolin Tsaro A Najeriya – Sanata Ndume

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Sojojin Najeriya a bakin aiki

__________

Najeriya ta daɗe tana fuskantar matsalolin tsaro, ta yadda a kullum al’amarin yake ƙara ta’azzara kuma daga dukkan alamu, lamarin ya gagari kundila.

A yankin Arewa, inda lamarin ya fi ta’azzara, an daɗe cikin masifar ‘yan Boko Haram, musamman a jihohin Arewa maso gabas, da suka haɗa da Borno, Yobe da sauransu.

A jihohin Arewa maso yamma kuwa, ‘yan bindigar daji sun daɗe suna satar mutane domin amsar kuɗin fansa da satar dabbobi da lalata amfanin gona.

A jihohin Arewa ta tsakiya ma, lamarin taɓarɓarewar tsaro ya ta’azzara. An daɗe ana samun rikice-rikicen da suka danganci na ƙabilanci, addini, makiyaya da manoma da ma na ‘yan bindiga masu satar mutane domin amsar kuɗin fansa.

A jihohin Kudu ma akwai matsalolin tsaro iri-iri, wannan kuwa sun haɗa da masu tada ƙayar baya, domin kafa ƙasar Biyafara da masu satar ɗanyen mai da ma masu satar mutane domin kuɗin fansa da sauransu.

Gwamnati a kullum tana kashe maƙudan kuɗaɗe, domin magance matsalolin tsaron amma kamar tana saran ruwa. To, ta yaya za a magance wannan babbar matsala ta tsaro da ta addabi al’ummar ƙasa? Sanata mai wakiltar Kudancin Borno, Mohammed Ali Ndume, a yayin tattaunawa da BBC Hausa a ƙarshen makon da ya gabata, ya bayyana wasu hanyoyi, waɗanda ya ce idan aka bi su, za a magance wannan matsala.

Sanata Ndume, a matsayinsa na jigon siyasa, wanda kuma ya fito daga Jihar Borno, inda aka daɗe ana fuskantar matsalar ‘yan Boko Haram ya bayyana hanyoyi huɗu kacal, waɗanda ya ce idan aka bi su, za a magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Gwamnan Jihar Borno, Umara Zulum, yayin da yake miƙe tallafi ga iyalan sojojin da suka rasa rayukansu a bakin aiki a kwanakin baya

Ya kawo kalmar Turanci ta “TEAM” a matsayin ƙunshiyar maganin matsalar tsaro a Najeriya. “T-Training (Horarwa), E-Equipment (Kayan Aiki), A-Ammunition (Makami) da kuma M-Motivation (Kyautatawa) su ne hanyoyi huɗu da ya kamata gwamnati ta bi, domin magance matsalolin tsaro da suka daɗe suna addabar ƙasarmu,” in ji Sanata Ndume.

Da yake ƙarin bayani dalla-dalla game da waɗannan hanyoyi huɗu, Sanatan ya ce, hanya ta farko ita ce, gwamnati ta dage sosai wajen horar da jami’an tsaro, domin su samu ƙwarewa sosai wajen hikimomi da dabarun daƙile aniyar masu laifi da gano su.

“Hanya ta biyu, ita ce gwamnati ta samar wa jami’an tsaro kayan aiki na zamani. Waɗannan sun haɗa da ingantattun motocin sufuri, na’urorin bincike na zamani da sauransu.” Sanatan ya ƙara da cewa, samar da kayan aiki na zamani ita ce hanya mafi sauƙi ta magance tsaro, wacce ta dogara da kimiyya da fasaha.

Hanya ta uku kuwa, Sanata Ndume ya ce, gwamnati ta zage damtse ta samar wa jami’an tsaro makaman yaƙi na zamani kuma wadatattu.

“Hanya ta huɗu kuwa,” in ji shi “ita ce a kula tare da kyautata rayuwar jami’an tsaro. Gwamnati ta tanadar wa jami’an tsaro da ingantacce kuma wadataccen albashi da alawus-alawus. A kula da lafiyarsu, ilimi da muhallinsu da na iyalansu.”

Sanatan ya sha alwashin cewa zai ci gaba da aikinsa na shawartar gwamnati da shugabannin tsaro, domin ganin an samar da ingantaccen tsaro a ƙasar nan.

__________

Previous Post

Double or Die: Thrills, Suspense and Puzzles

Next Post

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

Related Posts

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Babban Labari

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel
Babban Labari

Yadda Babban Jigon Jam’iyyar APC Daga Kano Ya Mutu A Otel

April 2, 2026
Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS
Babban Labari

Gwamnan Jigawa Ya Amso Walida Daga Hukumar DSS

February 26, 2026
Next Post
Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

NASIHA: Waƙen Ƙarfafa Gwiwa

NASIHA: Waƙen Ƙarfafa Gwiwa

July 22, 2023
Horror and Terror

Horror and Terror

September 4, 2024
Abubakar Dalhatu Zurmi: Zahirin Ɗan Kasa Nagari Mai Kishin Ƙasa

Abubakar Dalhatu Zurmi: Zahirin Ɗan Kasa Nagari Mai Kishin Ƙasa

October 10, 2025
AMBALIYA

AMBALIYA

September 11, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye
  • Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
  • MARTABAR MANZON ALLAH (SAW)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

April 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.